fidelitybank

Muna bincike game da jikkata mutane sanadin harbi a kasuwar Garki – DSS

Date:

Hukumar tsaron farin kaya ta DSS a Najeriya ta ce tana ci gaba da bincike, kuma za ta riƙa fitar da bayanai lokaci-lokaci, game da batun wasu mutane da aka jikkata sanadin harbin bindiga a kasuwar Garki.

A cikin wata sanarwa da ta fitar ranar Alhamis, hukumar ta ce mutanen da aka jikkata ranar 7 ga watan Satumba a Abuja, sun cancanci samun tallafi da kuma adalci.

DSS ta ce tuni ta kafa kwamiti a cikin gida don yin bincike, kuma jami’anta sun ziyarci mutum biyu da aka jikkata, waɗanda ke kwance suna jinya a asibitoci daban-daban.

Ba a dai saba jin hukumar DSS ta fito bainar jama’a, aƙalla tana nuna nadama a kan irin wannan lamari na zafin hannu da aka zargi wani jami’inta da aikatawa a kan wani ɗan ƙasa ba.

Sanarwar ta ce hukumar tana tuntuɓar dangin waɗanda lamarin ya ritsa da su, kuma za ta ci gaba da bibiyar halin da lafiyarsu take ciki.

Tuni da a cewarta, ta yi alƙawarin biyan kuɗin magani har ma ta ajiye wani ɓangare na kuɗin da aka nema, sannan a yayin ziyarar marasa lafiyan da jami’anta suka kai, hukumar ta bayyana aniyar mayar da su zuwa wani asibitinta da ke Abuja, don samun kulawa mafi inganci.

DSS ta ce ko da yake, hakan ba yana nufin amsa laifi ba ne, tun da a cewarta, har yanzu ba a kammala bincike ba, amma dai hukumar ta yi imani waɗanda abin ya faru da su, sun cancanci a tausaya musu, kuma sun cancanci samun adalci da tallafi.

Ta kuma ja hankulan ‘yan ƙasar da cewa DSS ba ta yi wani katsalandan ba, a binciken da ‘yan sanda ke yi, waɗanda ke tsare da jami’an da ake zargi da hannu a lamarin.

Jaridun Najeriya sun ambato wata sanarwa daga ‘yan sandan Abuja, tana cewa lamarin ya faru ne ranar Alhamis 7 ga watan Satumba a babbar kasuwar Garki, inda rigima ta kaure tsakanin ‘yan kasuwar da wasu mutane cikinsu har da wani jami’in hukumar DSS, da wani tela mai suna Muhammad Habibu.

Ta ce ‘yan sanda sun garzaya kasuwar saboda hargitsin da ya tashi, bayan samun rahoton cewa mutanen sun kutsa cikin kasuwar inda suka harbi wani tela mai suna Mubarak Mubarak.

“Wannan lamarin ya janyo har wasu matasa da suka fusata, sun yi yunƙurin auka wa jami’an DSS ɗin, amma ‘yan sanda suka shiga tsakani kuma suka kuɓutar da su. Ta ce a yayin hartsigin, an lalata wani ɓangare na ofishin ‘yan sanda.

nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp