fidelitybank

Muna aiki tukuru don bunƙasa noma a Najeriya – Tinubu

Date:

Shugaba Bola Tinubu na Najeriya ya tabbatar da cewa za a yi duk mai yiwuwa domin bunƙasa harkar noma da kuma samar da abinci a Najeriya.

Shugaba Tinubu ya bayyana haka ne a lokacin da yake ganawa da shugaban Brazil Inacio Lula Da Silva, a daidai lokacin da ake fara taron ƙungiyar ƙasashe ta Brics karo na 17.

A cewar sanarwar da mai taimaka wa shugaban kan harkokin yaɗa labarai Bayo Onanuga ya fitar, Tinubu ya ce wasu tsare-tsare mara kyau a baya sun taimaka wajen hana samun cigaba a ɓangaren noma a ƙasar.

Shugaban ya fada wa takwaransa na Brazil cewa tuni Najeriya ta fara aiwatar da wasu manufofi domin farfaɗo da tattalin arzikin ƙasar wanda zai yi gogayya da sauran duniya, musamman a ɓangaren noma.

Ya ƙara da cewa a shirye Najeriya take wajen kulla hulɗa da Brazil don ganin an ɗauki mataki nan take wajen ƙara bunƙasa samar da abinci.

“Za mu aiwatar da duk yarjejeniya da muka amince da Brazil, domin kawo gyara a ɓangaren kasuwanci, sufurin jiragen sama, makamashi, samar da abinci da kuma haƙar ma’adinai,” in ji Tinubu.

Ya kuma ce gwamnatinsa na ƙoƙari don bunƙasa harkar kiwon dabbobi.

A nasa ɓangare, shugaba Lula ya tabbatar da cewa za a aiwatar da duk wata yarjejeniya da aka cimma da Najeriya ba tare da ɓata lokaci ba, don ganin kyautatuwar tattalin arziki da kuma hulɗa tsakanin ƙasashen biyu.

naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp