fidelitybank

Muna aiki tukuru da jami’an tsaro wajen ceto daliban mu – Jami’ar Gusau

Date:

Mukaddashin shugaban jami’ar tarayya ta Gusau, Farfesa Aliyu Gadanga Tsafe, ya ce mahukuntan cibiyar da jami’an tsaro suna aiki kafada da kafada da su wajen ganin an ‘yantar da wasu daliban da aka sace kwanan nan a unguwar Damba da ke Gusau.

Da yake jawabi ga manema labarai a ofishinsa, Tsafe ya bayyana cewa ba a sace daliban a harabar jami’ar ba.

Ya kuma bukaci gwamnatin tarayya da masu zuba jari da masu hannu da shuni da su kawo agajin cibiyar ta hanyar samar da masauki ga dimbin daliban jami’ar saboda ayyukan ‘yan fashi da suka addabi cibiyar.

Tsafe ya dora laifin sace-sacen da ake yi a makarantar a kan rashin isassun katanga da kuma dakunan kwanan dalibai, inda ya ce mahukuntan makarantar ba su ji dadin yadda daliban ke zama a wajen harabar makarantar ba.

Mukaddashin shugaban jami’ar ya ce ana bukatar karin kudade domin kafa shingen kariya ga daliban da ma’aikatan makarantar.

“Ba mu da isasshen wurin kwana ga dalibai da ma’aikata a makarantar,” in ji shi.

Ku tuna cewa an yi garkuwa da wasu daliban Jami’ar a ranar Juma’ar da ta gabata.

general news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp