fidelitybank

Muna aiki gadan-gadan a kan sake fasalin tattalin arzikin Najeriya – Tinubu

Date:

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu, ya ce, gwamnatinsa tana aiki tuƙuru domin sake gyara tattalin arzikin ƙasar ta yadda za a mayar da hankali kan samar da manyan ayyuka tare da sabunta ayyukan more rayuwa.

Shugaba Tinubu ya bayyana haka jiya Alhamis lokacin da ya karɓi baƙuncin mambobin kwamitin gudanarwar jam’iyyar APC a jihar Legas.

A cewarsa, “ina sa ran za a fitarda kasafin kuɗi kowane lokaci daga yanzu, za ku ga yadda aka karkata kan manyan ayyuka, dole ne sabunta lalacewar ayyukan more rayuwa, mu kuma gyara hakan tare.”

Ya kuma bayyana damuwa game da yawan yaran da basa zuwa makaranta a ƙasar bayan rahoton baya-bayan nan da aka fitar.

“Ya zama dole mu magance wannan matsala ta hanyar samar da ƙarin makarantu da ɗiban malamai aiki da samar da tsarin ciyar da ɗalibai.” kamar yadda Tinubu ya bayyana.

Shugaba Tinubu ya ce dole ne dimokraɗiyya ta ci gaba kuma ta tafi da kowa da zummar magance talauci ta hanyar samar da damarmaki na aiki ga matasa da kuma inganta ilimin yaran Najeriya.

Ya ce yin haɗin gwiwa da ɓangarorin gwamnati da dama abu ne mai muhimmanci wajen ci gaban gwamnatinsu da kuma Najeriya.

A nasa ɓangaren, shugaban Jam’iyyar APC, Dr Abdullahi Umar Ganduje ya sanar da Tinubu cewa kwamitin gudanarwar jam’iyyar ya yi tsare-tsaren tabbatar da nasarar APC a zaɓen cike gurbin da ke tafe a watan Fabarairun 2024.

vanguardnewspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp