Wasu ‘yan Najeriya sun nuna sha’awar taimakawa kasar Ukraine ta shawo kan mamayar da sojojin Rasha suka yi wa kasar a makon jiya.
Dandazon matasn masu sha’awar taimakawa Ukraine sun yi wa ofishin jakadancin Ukraine kawanya a babban birnin tarayya Abuja.
Haka lamarin yake a kasashe da dama kamar yadda ‘yan Burtaniya, Amurkawa da kuma ‘yan Canada suma suka nuna sha’awar taimakawa Ukraine.
Matasan da suka yiwa ofishin jakadancin Ukraine da ke Abuja babban birnin Najeriya kawanya, sun kuma sanya sunayensu a cikin wata rajista da ofishin jakadancin ya bayar.
Jaridar Guardian ta rawaito cewa, jami’an ofishin jakadancin sun dakile yunkurin daukar hotunan mutane a bakin ofishin.
Sakatare na biyu na ofishin jakadancin Ukraine, Bohdan Soltys, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya kara da cewa har yanzu ba a dauki matakin da ya dace ba.