Jam’iyyar APC mai mulki ta bayyana cewa jam’iyyar a shirye take ta karbi mulki a jihar Enugu da sauran jihohin kudu maso gabas a shekarar 2023.
Sabon zababben mataimakin shugaban jam’iyyar APC na kasa reshen Kudu, Emma Eneukwu ne ya bayyana haka ranar Lahadi a Enugu lokacin da jam’iyyar ta karbe shi a filin jirgin saman Akanu Ibiam.
Mista Eneukwu, wanda ya yi jawabi ga taron ya bayyana cewa, APC ce za ta lashe zaben gwamna a daukacin jihar ta Kudu maso Gabas.
Ya kara da cewa lashe kujerar gwamnan Enugu ya fi muhimmanci ga jam’iyyar, saboda dabarun da take da shi a matsayin hedkwatar siyasar yankin.
Mataimakin shugaban jam’iyyar na kasa ya yi kira ga ‘ya’yan jam’iyyar na jihar Enugu da su kasance masu hadin kai ta yadda za su yi kokarin karbar mulki tare da samar da ingantacciyar shugabanci da zai sanya jin dadin ‘yan kasa a gaba.
“Lokaci ya yi da za mu karbe yankin Kudu maso Gabas gaba daya. Za mu yi hakan ne ta hanyar farawa daga gidan gwamnatin jihar Enugu.
“Mun zo ne domin mu kwace jihar Enugu; don baiwa Enugu sabon shugabanci.