Kyaftin din Wydad Athletic Club na Morocco, Yahya Jabrane ya ce tawagar ta je Najeriya domin doke Enyimba.
Tawagar Adil Ramzi za ta fafata da zakarun Najeriya a wasan daf da na kusa da na karshe a gasar cin kofin ƙungiyoyin Afrika.
Jabrane ya bayyana cewa Red Castle a shirye take domin karawa da zakarun Afirka sau biyu.
“Muna farin ciki da alfaharin kasancewa a nan a matsayin ƙungiya ta farko kuma tilo daga Morocco,” in ji Jabrane a wani taron manema labarai.
“Mun shirya don wasan a nan Najeriya da kuma Casablanca kuma za mu sanya komai don samun nasara.
“Babban lig ne, dukkan kungiyoyi suna da kyau kuma a shirye muke mu ba da mafi kyawun mu. Muna da damar samun sakamako mai kyau a karawar da Enyimba.”
Wasan da aka shirya gudanarwa a filin wasa na Godswill Akpabio International Stadium, Uyo, za a fara ne da karfe shida na yamma agogon Najeriya.