fidelitybank

Mun zo Najeriya don mu caskara Enyimba – Kyaftin ɗin Wydad

Date:

Kyaftin din Wydad Athletic Club na Morocco, Yahya Jabrane ya ce tawagar ta je Najeriya domin doke Enyimba.

Tawagar Adil Ramzi za ta fafata da zakarun Najeriya a wasan daf da na kusa da na karshe a gasar cin kofin ƙungiyoyin Afrika.

Jabrane ya bayyana cewa Red Castle a shirye take domin karawa da zakarun Afirka sau biyu.

“Muna farin ciki da alfaharin kasancewa a nan a matsayin ƙungiya ta farko kuma tilo daga Morocco,” in ji Jabrane a wani taron manema labarai.

“Mun shirya don wasan a nan Najeriya da kuma Casablanca kuma za mu sanya komai don samun nasara.

“Babban lig ne, dukkan kungiyoyi suna da kyau kuma a shirye muke mu ba da mafi kyawun mu. Muna da damar samun sakamako mai kyau a karawar da Enyimba.”

Wasan da aka shirya gudanarwa a filin wasa na Godswill Akpabio International Stadium, Uyo, za a fara ne da karfe shida na yamma agogon Najeriya.

nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...

A shirye nake na mutu don nasarar APC a 2027 – Orji Kalu

Sanatan Abia ta Arewa, Orji Uzor Kalu, ya bayyana...

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...
X whatsapp