Kocin Super Eagles, Jose Peseiro ya yaba wa ‘yan wasansa, saboda kwazon da suka nuna duk da rashin nasarar da kungiyar ta yi a hannun Algeria da ci 2-1 a daren Talata.
Najeriya ce ta fara cin kwallo ta hannun Terem Moffi a minti na tara da fara wasa, sai dai Desert Foxes sun yi fafatawa da Riyad Mahrez da Youcef Atal suka zura kwallayen.
Duk da cewa Super Eagles ta yi rashin nasara na uku a wasanni biyar da ta buga a karkashinsa, Peseiro bai damu da sakamakon wasan ba.
“Wasa ne mai kyau, sansanin ya nuna ingancin ‘yan wasanmu da kokarinsu na hadin gwiwa. Wasa ne mai wahala, Algeria kungiya ce mai kyau. ‘Yan wasanmu suna kokarin yin abin da na umarce su da su yi a horo,” Peseiro ya shaida wa NFF TV.
“Yana yiwuwa ku yi rashin nasara a kwallon kafa, ina bakin ciki mun yi rashin nasara. Ba na son yin rashin nasara a wasa, amma ina matukar farin ciki da kwazon ‘yan wasa na. Sun yi kyau a wasan.”
Peseiro, duk da haka, ya yi imanin cewa ƙungiyarsa za ta buƙaci inganta yanayin wasan da za su yi a wasannin gaba.
“Ba mu yi kyau ba wajen kai hari a wasu lokuta, ina ganin za mu iya yin abin da ya fi kyau. Za mu iya inganta wasanmu gaba daya,” in ji tsohon kocin Saudiyya da Venezuela.
“Muna yin kyaun tsaro amma za mu iya kara kai hare-hare da sarrafa kwallon,” in ji shi.