fidelitybank

Mun yi kokari amma an ci mu – Super Eagles

Date:

Kocin Super Eagles, Jose Peseiro ya yaba wa ‘yan wasansa, saboda kwazon da suka nuna duk da rashin nasarar da kungiyar ta yi a hannun Algeria da ci 2-1 a daren Talata.

Najeriya ce ta fara cin kwallo ta hannun Terem Moffi a minti na tara da fara wasa, sai dai Desert Foxes sun yi fafatawa da Riyad Mahrez da Youcef Atal suka zura kwallayen.

Duk da cewa Super Eagles ta yi rashin nasara na uku a wasanni biyar da ta buga a karkashinsa, Peseiro bai damu da sakamakon wasan ba.

“Wasa ne mai kyau, sansanin ya nuna ingancin ‘yan wasanmu da kokarinsu na hadin gwiwa. Wasa ne mai wahala, Algeria kungiya ce mai kyau. ‘Yan wasanmu suna kokarin yin abin da na umarce su da su yi a horo,” Peseiro ya shaida wa NFF TV.

“Yana yiwuwa ku yi rashin nasara a kwallon kafa, ina bakin ciki mun yi rashin nasara. Ba na son yin rashin nasara a wasa, amma ina matukar farin ciki da kwazon ‘yan wasa na. Sun yi kyau a wasan.”

Peseiro, duk da haka, ya yi imanin cewa ƙungiyarsa za ta buƙaci inganta yanayin wasan da za su yi a wasannin gaba.

“Ba mu yi kyau ba wajen kai hari a wasu lokuta, ina ganin za mu iya yin abin da ya fi kyau. Za mu iya inganta wasanmu gaba daya,” in ji tsohon kocin Saudiyya da Venezuela.

“Muna yin kyaun tsaro amma za mu iya kara kai hare-hare da sarrafa kwallon,” in ji shi.

fg spw news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...
X whatsapp