fidelitybank

Mun yi alkawarin kubutar da Daliban Kuriga – Sojoji

Date:

Rundunar sojin Najeriya ta yi alƙawarin kuɓutar da fiye da ɗalibai 200 da ƴanbindiga suka sace a baya-bayan nan a jihar Kaduna.

Da yake magana a wani taron manema labarai a Abuja game da ayyukan rundunar sojin a makonni biyu da suka gabata, Daraktan yaɗa labarai na rundunar tsaron, Manjo Janar Edward Buba ya ce sojojin a shirye suke su ceto ɗaliban ba tare da an rasa rai ba.

Ya kuma ɗora laifin sace ƴangudun hijira a kwanakin da suka gabata daga Gamboru-Ngala a jihar Borno kan rashin mutunta umarni inda suka fita daga sansanin domin neman itacen girki ba tare da sanar da jami’ai ba.

Tun dai bayan sace ɗaliban ne, shugaba Bola Tinubu ya umarci hukumomin tsaro su gano ƴanbindigar tare da kuɓutar da ɗaliban inda ya nanata cewa gwamnati ba za ta biya kuɗin fansa ba.

Bayan taron majalisar zartaswa na ranar Laraba ministan yaɗa labaran ƙasar Muhammad Idris ya bayyana hakan inda ya shaida wa ƴanjarida cewa shugaba Tinubu ya nanata umarnin tabbatar da kuɓuto ɗaliban da mayar da su ga iyalansu lami lafiya.

nigeria legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp