Mataimakin Sakataren Yada Labarai na Jam’iyyar APC mai mulki, Hon. Murtala Yakubu Ajaka, ya yaba da zaben tsohon Gwamnan Jihar Borno, Kashim Shettima, a matsayin abokin takarar Bola Tinubu a zaben 2023 mai zuwa.
Tinubu dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ya bayyana a ranar Lahadi cewa, Shettima ne zai zama mataimakinsa a 2023.
Tuni dai tikitin takarar Musulmi da Musulmi na jam’iyyar APC ya jawo ce-ce-ku-ce.
Tinubu ya ce, duk da cewa, akwai damuwa game da tikitin takarar Musulmi da Musulmi, amma ya zabi Shettima ne saboda tsohon Gwamnan Jihar Borno zai kawo kyakkyawan shugabanci ga ‘yan Najeriya ba tare da la’akari da addini ko kabila ba.
Da yake mayar da martani kan sanarwar, Ajaka, a wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin a Abuja, ya bukaci ‘yan Najeriya da su ga bayan ra’ayin addini da kabilanci.
Bayanin Ajaka ya kara da cewa, “Kyakkyawan halayen dan takararmu na mataimakin shugaban kasa, a wajen Sanata Kashim Shettima, ya sake jefa jam’iyyun adawa cikin daidaito.