fidelitybank

Mun yaba akan hukuncin kotu na sanya Hijabi ga daliban Legas – Kungiyar Musulmai

Date:

Kungiyar dalibai musulmi ta kasa reshen jihar Legas (MSSN) ta yaba da hukuncin da kotun koli ta yanke wanda ya dace da amfani da hijabi a makarantun mallakar gwamnati a jihar.

A hukuncin da kotun kolin ta yanke a ranar Juma’a, ta tabbatar da hakkin dalibai mata musulmi na saka hijabi a makarantun firamare da sakandare na gwamnati a Legas.

Da yake mayar da martani kan hukuncin, shugaban kungiyar MSSN a jihar Legas, Miftahudeen Thanni, ya bayyana farin cikinsa da cewa dalibai mata musulmi yanzu za su iya sanya hijabi zuwa makaranta ba tare da tsangwama ba.

A wata sanarwa da ta fitar jim kadan bayan kotun kolin ta yanke hukuncin, Thanni ya ce hukuncin ya karawa daliban kwarin gwiwa a bangaren shari’a.

Ya ce, “Hukuncin kawai yana nufin cewa duk da cewa hijabi ba ya wajaba a makarantun Legas, amma daliban musulmin da ke son sanya shi suna da ‘yancin yin hakan kuma a bisa doka.

“Mu kungiya ce mai bin doka kuma za mu ci gaba da bin dokar kasa. Mun yaba da hukuncin. Matsayin doka ya fito fili a kan batun. Wannan al’amari ya sake tabbatar mana da cewa duk bege bai rasa nasaba da samun al’umma ta gari.

“Kada gwamnati ta yi yaki da matasan da suka zabi suturce tsiraicinsu tare da karfafa masu tafiya tsirara da aikata haramun a bainar jama’a.”

mmm.nnn.

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp