fidelitybank

Mun yaba akan hukuncin kotu na sanya Hijabi ga daliban Legas – Kungiyar Musulmai

Date:

Kungiyar dalibai musulmi ta kasa reshen jihar Legas (MSSN) ta yaba da hukuncin da kotun koli ta yanke wanda ya dace da amfani da hijabi a makarantun mallakar gwamnati a jihar.

A hukuncin da kotun kolin ta yanke a ranar Juma’a, ta tabbatar da hakkin dalibai mata musulmi na saka hijabi a makarantun firamare da sakandare na gwamnati a Legas.

Da yake mayar da martani kan hukuncin, shugaban kungiyar MSSN a jihar Legas, Miftahudeen Thanni, ya bayyana farin cikinsa da cewa dalibai mata musulmi yanzu za su iya sanya hijabi zuwa makaranta ba tare da tsangwama ba.

A wata sanarwa da ta fitar jim kadan bayan kotun kolin ta yanke hukuncin, Thanni ya ce hukuncin ya karawa daliban kwarin gwiwa a bangaren shari’a.

Ya ce, “Hukuncin kawai yana nufin cewa duk da cewa hijabi ba ya wajaba a makarantun Legas, amma daliban musulmin da ke son sanya shi suna da ‘yancin yin hakan kuma a bisa doka.

“Mu kungiya ce mai bin doka kuma za mu ci gaba da bin dokar kasa. Mun yaba da hukuncin. Matsayin doka ya fito fili a kan batun. Wannan al’amari ya sake tabbatar mana da cewa duk bege bai rasa nasaba da samun al’umma ta gari.

“Kada gwamnati ta yi yaki da matasan da suka zabi suturce tsiraicinsu tare da karfafa masu tafiya tsirara da aikata haramun a bainar jama’a.”

thisday nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojoji sun hallaka ƴanbindiga da dama a Plateau

Rundunar sojoji ta ce, ta kashe ƴanbindiga da dama...

Duk wani tuggun ku Atiku da El-Rufa’i ba za ku iya kayar da Tinubu ba – Bwala

Fadar shugaban kasa ta yi watsi da kokarin da...

Mutuwar Dantata ta girgiza kasa baki daya – Tinubu

Shugaban kasa Ahmad Bola Tinubu ya bayyana Alhaji Aminu...

Wike ya caccaki Rotimi a kan jam’iyyar ADC

Ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike, ya caccaki tsohon...

Tsige ni daga mukamin Wazirin Gaya ba a kan doka ba ne – Usman Alhaji

Tsohon sakataren gwamnatin jihar Kano, Alhaji Usman Alhaji, ya...

Gini mai bene uku ya danne Mutane a jihar Legas

Wani gini mai bene uku ya rufta a unguwar...

Kotu ta daure Matashi dan Tiktok da ya ke sanya rigar mama

Wata kotu a jihar Kano, ta yanke wa wani...

Peter Obi ka gaggauta ficewa daga jam’iyyar mu nan da awa 48 – Labour Party

Bangaren jam’iyyar Labour da Julius Abure ke jagoranta, ya...

Lakurawa sun kashe Mutane 15 a Sokoto

Wasu da ake zargin mambobin ƙungiyar Lakurawa ne sun...

Dan wasan Liverpool Diago Jota da Kaninsa sun mu a hadarin mota

Ɗan wasan ƙwallon ƙafar Liverpool kuma ɗan ƙasar Portugal,...

Mun shirya tunkarar APC a 2027 – ADC

A ranar Laraba ne manyan ƴan adawar siyasa suka...

Mun dagulawa Iran lisafi na tsawon shekaru biyu a nukiliyar ta – Amurka

Ma'aikatar tsaron Amurka ta ce bayannan leken asirinta ya...
X whatsapp