Gwamnatin jihar Bauchi ta amince da Naira miliyan 100 domin gudanar da gasar karatun Alkur’ani ta kasa karo na 36 na shekarar 2022 a jihar.
Gwamna Bala Mohammed ya bayyana hakan a yayin bikin rantsar da mambobi 57 na kwamitin shirya gasar a ranar Asabar, 12 ga watan Maris, a garin Bauchi.
Kamfanin dillancin labarai na kasa NAN ya rawaito cewa, an shirya gudanar da gasar ta kasa a Bauchi daga ranar 18-20 ga watan Maris.
Mohammed ya ce, wannan ne karo na uku da jihar Bauchi za ta karbi nauyin gasar tun: “Ina son bayyana cewa, ma’aikatar harkokin addini, tare da hadin gwiwar jami’ar Usman Dan Fodio ta Sokoto da sauran hukumomin gwamnati sun gabatar da kasafin kudi na Naira miliyan 153 na gasar. Gwamnatin jihar za ta samar da Naira miliyan 100 ga wannan kwamitin domin a samo sauran a wani wurin.”