fidelitybank

Mun tuntubi Saudiyya a kan karancin bizar Najeriya – NAHCON

Date:

Hukumar alhazai ta kasa NAHCON, ta ce ta rubutawa Saudiyya a hukumance, inda ta sanar da ita halin da ake ciki game da ƙarancin biza ga ‘yan ƙasar da suke son zuwa umrah.

NAHCON ɗin ta ce ta yi wa hukumomin Saudiyyar bayanin illar rashin bai wa kamfanonin shirya tafiye-tafiyen bizar a yanayin da ake ciki.

Cikin wata sanarwa da hukumar NAHCON ta fitar ta bayyana irin kalubalen da ‘yan Najeriya ke fama wajen samun bizar shiga saudiyya don gudanar da ibadar umrah a wanann wata na Ramadan a matsayin abin takaici.

Dumbin maniyyata wadanda suka shirya tafiya umrah tuntuni tsakaninsu da kamfanonin shirya tafiye-tafiye, suna ci gaba da bayyana takaicinsu da rashin samun biza daga hukumomin Saudiyya.Adadin masu zuwa Umrah a lokacin watan Ramadan galibi ya kan fi na sauran lokuta saboda kwadayin dacewa da tarin ladan da ke tattare da yin ibadar a cikin watan na azumi, inda miliyoyin musulmi daga kasashe da dama na duniya ke zuwa yin umarah.

naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...
X whatsapp