Shugaban Kenya, ya ce, kasarsa ba za ta saba a’idar biyan duk wani bashi da ta ci ba saboda tsananin matsalar tattalin arziki da take ciki.
William Ruto ya faɗa wa manema labarai cewa Kenya ta dakatar da cin duk wani bashi daga yanzu.
A lokacin da gwmnatinsa ta karbi mulki a watan Satumba na shekarar da ta kare, ta ce za ta rage cin bashi mai tsada na gudanar da harkokin da suka jiɓanci kasuwanci.
A maimakon haka za ta karkata ga cibiyoyi da hukumomi masu bayar da bashi mai sauki kamar Bankin Duniya.
Ita ma Kenya, kamar sauran kasashen Afirka, na fuskantar haɗarin raguwar kima ko karfinta na samun rance, saboda katutun bashi da ke ta karuwa a kanta da kuma kudin ruwa na duniya da shi ma yake cirawa.