fidelitybank

Mun tantance Daliban da za su karatu waje su 1,1010 – Gwamnatin Kano

Date:

Gwamnatin jihar Kano ta kammala shirin fara daukar nauyin daliban manyan makarantu 1,010 a gida da waje a kashi na farko na tallafin karatun da za ta yi.

Kwamishinan ilimi mai zurfi na jihar Dr. Yusif Ibrahim Kofar Mata, ne ya bayyana haka a taron manema labarai da aka gudanar a ofishin kwamishinan yada labarai.

 

Da yake jawabi ga manema labarai, Kwamishinan ya bayyana cewa an kafa kwamitin tantancewa na sake dawo da shirin daukar nauyin daliban da suka kammala karatu a Kano domin samun digiri na biyu a jami’o’in cikin gida da na ketare, an kafa tare da kaddamar da kwamitin a ofishin sakataren gwamnatin jihar.

Ya kara da cewa, kwamitin ya karbi takardun neman shiga cikin shirin daga mutane sama da 1200, Kuma ya zuwa yanzu an tantance sama da mutane 800, kuma har yanzu ana cigaba da tantancewar kuma za a fitar da cikakkun bayanai na wadanda suka sami nasara nan ba da jimawa ba.

“Yana da matukar muhimmanci a sanar da al’ummar Kano cewa, dawo da wannan shiri da gwamnatin Abba Kabir Yusif ta yi, ba wai kawai don samawa ‘yan jihar Kanon takardar shaidar kammala digiri ba, a’a, a’a, a’a, shirin zai karawa matasanmu kwarin gwiwa da kuma kara samun damammaki a fannoni daban-daban waɗanda wataƙila za su iya taimakawa wajen sauya matsayin jiharmu a idanu duniya”.

Kwamishinan wanda kuma shi ne sakataren kwamitin maido da manufofin Kano na bayar da tallafin karatu ya bayyana cewa maido da manufar bayar da tallafin karatu ga ‘yan asalin jihar Kano don yin manyan digiri a ciki da wajen kasar nan an yi shi ne da niyyar bunkasa rayuwar al’ummar Kano da Nigeria baki daya. In ji Kadaura.

legit news 
nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...
X whatsapp