Gwamnatin jihar Kano ta kammala shirin fara daukar nauyin daliban manyan makarantu 1,010 a gida da waje a kashi na farko na tallafin karatun da za ta yi.
Da yake jawabi ga manema labarai, Kwamishinan ya bayyana cewa an kafa kwamitin tantancewa na sake dawo da shirin daukar nauyin daliban da suka kammala karatu a Kano domin samun digiri na biyu a jami’o’in cikin gida da na ketare, an kafa tare da kaddamar da kwamitin a ofishin sakataren gwamnatin jihar.
Ya kara da cewa, kwamitin ya karbi takardun neman shiga cikin shirin daga mutane sama da 1200, Kuma ya zuwa yanzu an tantance sama da mutane 800, kuma har yanzu ana cigaba da tantancewar kuma za a fitar da cikakkun bayanai na wadanda suka sami nasara nan ba da jimawa ba.
“Yana da matukar muhimmanci a sanar da al’ummar Kano cewa, dawo da wannan shiri da gwamnatin Abba Kabir Yusif ta yi, ba wai kawai don samawa ‘yan jihar Kanon takardar shaidar kammala digiri ba, a’a, a’a, a’a, shirin zai karawa matasanmu kwarin gwiwa da kuma kara samun damammaki a fannoni daban-daban waɗanda wataƙila za su iya taimakawa wajen sauya matsayin jiharmu a idanu duniya”.
Kwamishinan wanda kuma shi ne sakataren kwamitin maido da manufofin Kano na bayar da tallafin karatu ya bayyana cewa maido da manufar bayar da tallafin karatu ga ‘yan asalin jihar Kano don yin manyan digiri a ciki da wajen kasar nan an yi shi ne da niyyar bunkasa rayuwar al’ummar Kano da Nigeria baki daya. In ji Kadaura.