fidelitybank

Mun soke rijista zabe kashi 40 ciki 100 – INEC

Date:

Hukumar zaɓe ta ƙasa INEC, ta ce, kashi 40 cikin 100 na sabbin waɗanda ta yi wa rajistar katin jefa ƙuri’a ɗalibai ne, tana mai cewa ta soke rajista kusan miliyan uku da suka saɓa wa ƙai’dojin hukumar.

Shugaban hukumar ta Independent National Electoral Commission (INEC) Farfesa Mahmood Yakubu ya ƙara da cewa kashi 76 cikin 100 na masu zaɓe a ƙasar matasa ne.

A cewarsa yayin wani taro da jam’iyyun siyasa a Abuja ranar Laraba, an samu ƙarin masu katin jefa ƙuri’a 9,518,188 a kan 84,004,084 da ake da su, kuma a yanzu rajistar farko-farko ta nuna cewa jimillar adadinsu ya kai 93,522,272.

“Bayan kammala aikin, mutum 12,298,944 ne suka yi rajistar. Amma tun tuni mun sha faɗa cewa hanyoyinmu na tsaftace rajistar masu inganci ne,” in ji shi.

“Bayan mun tantance bayanan ta hanyar amfani da tsarin Automated Biometric Identification System (ABIS), mun gano 2,780,756 (kashi 22.6 cikin 100) ba su cancanta ba kuma muka goge su. Cikinsu akwai waɗanda suka yi sau biyu, da yaran da ba su kai ba, da kuma ma na boge waɗanda ba su cika ƙa’idojinmu ba.”

A watan Fabarairu na 2023 ne INEC za ta gudanar da babban zaɓe a Najeriya, inda ‘yan ƙasa za su zaɓi sabon shugaban ƙasa da gwamnonin jiha da ‘yan majalisar jiha da na tarayya.

legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kashe kwamandan Boko Haram a tafkin Chadi

Sojojin Jamhuriyar Nijar sun sanar da kisan wani jagoran...

Hisbah za ta yi wa ‘yan Daban Kano aure

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta sanar da wani...

Ganduje ya dawo Najeriya bayan ya shafe wata guda a Landan

Tsohon shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Dr. Abdullahi Ganduje,...

Barrister Sa’idu ya kama aiki bayan ya maye gurbin Muhyi Magaji

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya rantsar...

An ceto Mutane 26 da kwale-kwale ya kife da su a Sokoto

An samu nasarar ceto mutum 29 bayan hatsarin kwale-kwale...

An ceto Mutane 26 da kwale-kwale ya kife da su a Sokoto

An samu nasarar ceto mutum 29 bayan hatsarin kwale-kwale...

Barau zai mayar da filin wasan BUK na zamani

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya...

Jami’ar Bayero ta Kano ta yi sabon shugaba

Farfesa Haruna Musa, ya karɓi ragamar shugabancin jami’ar Bayero...

Gwamnatin Kano ta amince Barau FC ta yi wasa a filin Sani Abacha

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da kungiyar kwallon kafa...

Gwamnatin Tinubu na takalar Kwankwaso da fada – Buba Galadima

Jigo a jam'iyyar NNPP, kuma na hannun tsohon gwamnan...

Newcastle United ta dauki dan wasan tsakiya Jacob daga Aston Villa

Newcastle United ta sanar da daukar dan wasan tsakiya...
X whatsapp