fidelitybank

Mun shirya tsaf na tunkarar Algeria – Troost-Ekong

Date:

Mataimakin kyaftin din Super Eagles, William Troost-Ekong, ya bayyana cewa kungiyar ta shirya tsaf domin buga wasan sada zumunta da Algeria.

Zakarun Afirka sau uku za su fafata da kungiyar Algeria B a wasan sada zumunta na farko a filin wasa na Mohamed Hamlaoui, Constantine ranar Juma’a.

Wasan sada zumunci na biyu da Riyad Mahrez ya jagoranci Desert Foxes ana biya ne a filin wasa na Miloud Hadefi, Oran mako mai zuwa Talata.

Super Eagles dai ta samu nasara a wasanni biyun da ta buga da Saliyo kuma Sao Tome and Principe da Troost-Ekong na fatan kungiyar za ta ci gaba da samun nasara.

“Muna so mu yi kokarin lashe dukkan wasanni da kuma inganta a kowane fanni, muna wasa da Algeria, daya daga cikin manyan kungiyoyi a Afirka,” mai tsaron gida Watford ya shaida wa NFF TV.

Ya kara da cewa “Dole ne mu nuna musu girmamawa, amma a lokaci guda, duk da cewa wasan sada zumunci ne, za mu yi kokarin samun nasara a wasan da kuma shirya kanmu a wasannin share fage da za su zo nan gaba.”

Babban kociyan kungiyar, Jose Peseiro ya gayyaci sabbin ‘yan wasa da dama don buga wasannin sada zumunta sakamakon rashin wasu taurarin dan wasa na yau da kullun.

Troost-Ekong ya yi imanin cewa wata dama ce ga sabbin ‘yan wasa su nuna ajin su a matakin kasa da kasa.

“Yana da babbar dama ga sababbin ‘yan wasa su nuna kansu da kuma dukanmu mu haÉ—u tare da fahimtar abin da kocin yake bukata daga gare mu,” in ji shi.

www.nigeriannewspapers.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...

Mukarraban gwamnati ba zan lamunci dabi’ar zubar da kima ta ba – Abba

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya gargaÉ—i masu...

WAEC ta sake bude shafinta don duba jarabawar bana

Hukumar shirya jarabawar Afirka ta Yamma (WAEC) ta bayyana...

Indonesia za ta gina asibiti dubu biyu ga FalasÉ—inawa

Indonesia ta sanar da cewa za ta kafa wata...

Lauyan Sowore ya bukaci a sake shi cikin gaggawa

Lauyoyin ffitaccen É—an gwagwarmayar nan kuma É—an jarida, Omoyele...

Najeriya da Indiya za su haɗa kai na yaƙi da fataucin miyagun ƙwayoyi

Hukumar hana sha da fatauncin miyagun ƙwayoyi ta Najeriya,...

Jihohi 19 da za a yi kwana 9 a na ruwan sama harda Kano – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta yi hasashen za a shafe kwana...

Tinubu ya mika sakon ta’aziyya bisa rasuwar matar MKO Abiola

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya miƙa saƙon ta'aziyyarsa bisa...

Abubuwan da Kwamiti ya gano a wajen Kwamishina mai murabus na Kano

A ranar Litinin ne kwamitin binciken badaƙalar belin Danwawu,...
X whatsapp