fidelitybank

Mun shirya tsaf domin gudanar da zanga-zanga a Kano – Kungiyoyin Kwadago

Date:

Kungiyoyin kwadago Najeriya NLC da TUC reshen jihar Kano, sun bayyana cewa a shirye suke su shiga zanga-zangar adawa da shirin gwamnatin tarayya na kara farashin man fetur a fadin kasar.

Da yake jawabi ga mambobin majalisar a jiya, shugaban kungiyar NLC reshen Kano, Kabiru Minjibir, ya bayyana cewa an shirya gudanar da wata babbar zanga zanga a ranar 27 ga watan Janairun 2022, bisa bin umarnin hukumar ta kasa.

Minjibir, wanda ya koka da rashin daidaiton manufofin gwamnati, ya dage cewa, ma’aikatan Najeriya za su sha wuya, domin hana janye tallafin man fetur, wanda a karshe zai iya haifar da hauhawar farashin kaya.

Ya ce: “Mun umurci mambobinmu da su fara gangami tun daga ranar 27 ga watan Janairu, 2022, domin gudanar da zanga-zanga a fadin jihohi 36 na tarayya, na nuna rashin jin dadinmu kan shirin janye tallafin man fetur. Kuma a shirye muke mu ci gaba da gudanar da zanga-zangar lumana. Amma idan aka yi la’akari da yanayin siyasar Kano, zanga-zangar tamu za ta kasance a tsare ne, wanda zamu taru ne a filin sukuwa, sannan mu yi tattaki zuwa gidan gwamnati”. In ji Kwamrade Kabiru.

A nasa jawabin shugaban TUC na Kano, Mansur Adamu, ya shaida wa manema labarai cewa, ‘yan kasuwa masu zaman kansu sun shirya tsaf domin shiga zanga-zangar ta NLC.

 

latest news in nigeria today 2022 punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp