Hukumar zabe mai zaman kanta INEC, ta ce, ta kammala shirin gudanar da zaben gwamnan jihar Osun.
Hukumar ta ce, ta yi hakan ne don gudun samun wasu matsaloli a ranar zaben.
INEC, ta ce, yayin da ya rage lokaci kalilan a fara kada kuri’a a fadin jihar, tuni ta rarraba takardun zabe ga kananan hukumomin jihar 30.
A gaban jami’an tsaro aka kammala rarraba kayayyakin zabe masu muhimmanci.
Hajiya Zainab Aminu, jami’a ce a hukumar wadda kuma ta je Osogbo don ganin yadda zaben zai wakana, kuma ta shaida wa BBC cewa,Mun hukumar ta yi nasarar rarraba kayayyakin ne da suka hada da takardar kada kuri’a da kuma takardar rubuta sakamakon zabe.
Hajiya Zainab, ta ce sai da hukumar ta INEC, ta fara aikewa da kayan zaben ga kananan hukumomin da ke da nisa saboda su isa da wuri har a samu a rabasu zuwa gundumomi daga nan kuma sai rumfunar zabe.