fidelitybank

Mun shirya baiwa Tinubu taimako ya kawo karshen rikici – KACRAN

Date:

Kulen Allah Cattle Rearers Association of Nigeria, KACRAN, ta yi kira ga zababben shugaban kasa Bola Tinubu da ya lalubo hanyar warware rikicin makiyaya da manoma a Najeriya da ke haddasa asarar rayuka da dukiyoyi.

Shugaban kungiyar na kasa, Khalil Mohammad Bello ne ya yi wannan kiran a cikin wata sanarwa da ya sanyawa hannu kuma ya mika wa DAILY POST a Damaturu babban birnin jihar Yobe.

Bello, yayin da yake taya Tinubu da mataimakinsa mai jiran gado, Kashim Shettima murna, ya gabatar da cewa nasarar da suka samu wata alama ce ta kwarin gwiwa da amincewa da miliyoyin ‘yan Najeriya suka yi musu.

“Muna kira gare su da kyar da su yi amfani da sabbin ofisoshi nagari a matsayinsu na Shugaban kasa da Mataimakin Shugaban Tarayyar Najeriya don samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali tsakanin makiyaya da manoma ta kasa domin su zauna lafiya,” inji shi.

A yayin da ta ke ba su tabbacin goyon bayan KACRAN da hadin kan su wajen magance duk wasu rikice-rikicen da suka dabaibaye kasar nan, kungiyar ta kuma tabbatar wa Tinubu cewa, samar da mafita mai dorewa kan rikicin makiyaya da manoma zai taimaka ba karamin mataki ba wajen magance kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta.

A cewar Bello, KACRAN a shirye take ta bayar da duk wani taimako da zai kawo karshen rikicin musamman a yankin arewacin kasar.

besda

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp