Hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa NEMA, ta sake gano wasu gawarwaki 13 daga cikin kwale-kwalen da ya taso daga Mile 2 zuwa Ibeshe da ke wajen birnin Legas a ranar Asabar.
Mista Ibrahim Farinloye, Ko’odinetan shiyyar Kudu-maso-Yamma, NEMA ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi a Legas.
Ya ce ya zuwa yanzu an gano gawarwakin mutane 17 daga aikin ceto wadanda suka bata.
“Da daren jiya, an sake gano wasu gawarwaki biyu baya ga biyun da aka gano tun da safe. Da wannan, ya zama jimillar gawarwaki 17 da aka gano,” inji shi.
Farinloye ya ce, masu safarar jiragen ruwa ba bisa ka’ida ba da ke zirga-zirga a magudanar ruwa fiye da sa’o’in da aka kayyade a hukumance sun yi sanadiyar mutuwar da ba za a iya kaucewa ba.