fidelitybank

Mun rage wa ɗalibai kuɗin makaranta kaso 50 cikin 100 saboda halin rayuwa – Gwamnatin Kano

Date:

Gwamnatin jihar Kano ta ce, ta rage wa daliban manyan makarantun jihar kudin makaranta da kashi 50 cikin 100.

Gwamnan jihar Alhaji Abba Kabir Yusuf, ne ya bayyana hakan a shafukansa na sa da zumunta a daren Litinin.

Gwamnan ya bayyana haka ne bayan ya karbi bakuncin shugabannin makarantun gaba da sakandire mallakin gwamnatin jihar.

Abba Kabir, ya ce ya ba da umarnin rage kudin makaratar nan take.

Hakan dai na nufin daga yanzu daliban Kano da suke karatu a makarantun gaba da sakandare mallakin gwamnatin jihar za su rinka biyan rabin kudin da suke biya ne.

Kwamishinan ma’aikatar ilimi mai zurfi ta jihar, Dakta Yusuf Ibrahim Kofar Mata, ya shaida wa BBC cewa, gwamnatin jihar ta duba yanayin kuncin rayuwa da ake ciki wanda abin ya ta’azara bayan janye tallafin man fetir.

Ya ce, a yanzu abubuwa sun kara tsada kamar kudin mota da kayan abinci da ma sauran abubuwan da ake ta’ammali da su na yau da kullum.

Kwamishinan ya ce, ” A duk lokacin da aka samu yanayi na tsadar kayan abinci, to iyaye kan sha wuya wajen biyawa ‘ya’yansu kudin makaranta, to wannan dalilin ne ya sa gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf, ya ce bari a nemi hanyoyin saukakawa iyaye da ma dalibai a wannan hali da ake ciki shi ya sa ma ya ce bari abi dukkan manyan makarantu mallakin gwamnatin jihar su takwas a rage kudinsu ta yadda iyayen yara da adlibai za su biya rabi gwamnati ta cire sauran rabin”

Dakta Yusuf Ibrahim Kofar Mata, ya ce an dauki wannan mataki ne don a tallafawa ilimi da farfado da shi, sannan kuma ya zama wani tallafi a wannan shekarar wajen rage radadin rayuwar ma da ake ciki.

Kwamishinan ya ce sun shirya tsaf don ganin komai ya tafi daidai a wannan tsari.

the nation newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp