fidelitybank

Mun rage karfin ‘yan ta’adda a Katsina da kaso 70 – Radda

Date:

Gwamna Dikko Radda na jihar Katsina ya ce, gwamnatinsa ta rage yawan ‘yan fashi da makami zuwa kashi 70 cikin 100 a cikin shekara daya.

A cewar Radda, hakan ya biyo bayan yadda aka samu hadin kai tsakanin jami’an tsaron gida da na jami’an tsaro na yau da kullum a fadin jihar.

Radda, wanda ya kai ziyarar aiki a Yola, ya bayyana hakan ne a wata hira da manema labarai a ranar Asabar.

Ya ce, “Lokaci ya yi da za a saka ‘yan sandan jihohi a cikin yaki da rashin tsaro a kasar nan.

“Mun rage yawan ‘yan fashin zuwa kusan kashi 60 zuwa 70 cikin 100. Abin da muke gani a yanzu shi ne irin hauka da ‘yan fashin ke bi na zuwa kauyukan da ke da wuyar isa ga dazuzzuka, suna kona gidaje da kashe mutane.

“Mun kirkiro dabarun yakar ta.”

Radda ya ci gaba da bayanin cewa galibin kasashe masu tasowa suna da ‘yan sandan jihohi da ke tsaron rayuka da dukiyoyi.

Ya bukaci gwamnatoci a dukkan matakai da su baiwa ilimi fifiko domin ci gaban kasa.

Radda ya ce, “Wannan zai ba da dama ga masu karamin karfi, don samun ilimi mai inganci a kowane mataki.”

sun news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp