fidelitybank

Mun lalata sama da gine-gine 200 a zirin Gaza – Isra’ila

Date:

Rundunar sojin Isra’ila a ranar Talata, ta ce, an kai hare-hare sama da 200 a cikin dare, ciki har da ma’ajiyar makamai da Hamas ke amfani da shi da kuma wasu cibiyoyi na Islamic Jihad, wata kungiyar Islama ta Falasdinu.

Daruruwan Falasdinawa masu kai hari ne suka tsallaka kan iyakar kasar zuwa Isra’ila a ranar Asabar.

Kimanin mutane 900 ne aka kashe a kisan kiyashin da ya biyo baya.

A Be’eri, wani kibbutz da ke kudancin Isra’ila, an gano gawarwaki sama da 100 a ranar Litinin bayan da sojoji suka sake kwace iko da yankin.

Mayakan Hamas sun yi garkuwa da akalla mutane 150 tare da mayar da su Gaza da suka hada da mata da kananan yara da kuma tsofaffi kamar yadda wani bincike da Isra’ila ta gudanar.

Sai dai kuma kungiyar Hamas ta yi barazanar kashe wani mutum daya da ta yi garkuwa da shi kan duk wani harin ba-ta-baci da Isra’ila ta kai kan fararen hula a Gaza.

A cewar rundunar sojin Isra’ila, ya zuwa yanzu an gano gawarwakin ‘yan ta’adda 1,500 a yankin na Isra’ila.

Hare-hare masu yawa da Isra’ila ta kai a zirin Gaza sun kashe mutane akalla 687 tare da jikkata wasu fiye da 3,800.

vgn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp