fidelitybank

Mun kuɓutar da mutane bakwai a Binuwai – Sojoji

Date:

Dakarun Exercise Enduring Peace na uku sun kubutar da wasu mutane bakwai da aka yi garkuwa da su a yankin Igaji da ke karamar hukumar Ohimini a jihar Benue.

Sojojin bataliya ta 72 da ta 401 a wani samame na hadin guiwa da ‘yan sa kai na al’umma sun cimma wannan nasara ne bayan da suka kaddamar da neman wadanda aka sace a ranar 9 ga watan Oktoba yayin da wasu daga cikinsu aka ce za su je gona.

Mai baiwa gwamna Hyacinth Alia shawara kan harkokin tsaro Joseph Har ne ya bayyana hakan a jiya a garin Makurdi, inda yace ceton ya biyo bayan wasu amintattun bayanan sirri da aka samu tun farko dangane da motsin wasu masu garkuwa da mutane a kusa da yankin Igaji.

Har ya ce, “Sojoji tare da hadin gwiwar Civilian Joint Task Force (CJTF) sun mayar da martani cikin gaggawa, inda suka garzaya yankin domin neman wadanda aka yi garkuwa da su tare da ceto mutane bakwai.”

Ya ci gaba da bayyana cewa, masu laifin da suka ga sojojin sun yi ta rugujewa suna barin wadanda aka yi garkuwa da su saboda karfin karfin sojojin.

Wadanda aka ceto sun hada da James Ebeh dan shekaru 19; Mary Ejeh, 40; Flora Alfa, 32; Maryamu Yahaya, 27; Ogumula Lahadi, 18; Fidelis Ogumala, 55; da Stephen Onihi mai shekaru 43.

Mai ba da shawara kan harkokin tsaro ya kara da cewa an mika wadanda aka ceto ga hakimin kauyen, Peter Ottoh Adakole, a gaban shugaban matasan, Iduma Fidelis, da sauran su bayan an kai su babban asibitin Otukpo domin kula da lafiyarsu.

sun newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp