fidelitybank

Mun kori ɗan takarar gwamnan Jigawa – ADC

Date:

Jam’iyyar African Democratic Congress, ADC, ta kori dan takararta na gwamna a jihar Jigawa, Muhammad Sani Gumel, bisa zargin cin zarafin jam’iyya.

Shugaban riko na jam’iyyar a jihar Jigawa Kabiru Hussaini ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Dutse babban birnin jihar.

Ya ce, an kori dan takarar gwamnan ne saboda sayar da jam’iyyar ga jam’iyyar All Progressives Congress, APC.

Karanta Wannan: Ba mu haɗe da kowacce jam’iyya ba a Kaduna – ADC

Kabiru Hussaini ya bukaci daukacin ‘yan jam’iyyar da su marawa dan takarar gwamna na jam’iyyar PDP, Mustapha Sule Lamido baya.

“Muna umurtar dukkan magoya bayan jam’iyyar mu da su marawa dan takarar gwamna na PDP goyon baya domin PDP ce kadai za ta iya ceto jihar daga rugujewa baki daya,” in ji shi.

Ɗan takarar gwamnan jihar ADC Muhammad Sani Gumel ya janye takararsa ya koma APC.

Da yake mayar da martani, dan takarar gwamna na jam’iyyar ADC Muhammad Sani Gumel, ya ce mukaddashin shugaban jam’iyyar ba shi da hurumin korarsa daga jam’iyyar.

Ya ce hedkwatar kasa ta kori mukaddashin shugaban jam’iyyar ne a ranar 22 ga Satumba, 2022 kuma hukumar INEC, IPAC, da hukumomin tsaro ba su amince da shi ba.

taraba state today news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...
X whatsapp