Jam’iyyar African Democratic Congress, ADC, ta kori dan takararta na gwamna a jihar Jigawa, Muhammad Sani Gumel, bisa zargin cin zarafin jam’iyya.
Shugaban riko na jam’iyyar a jihar Jigawa Kabiru Hussaini ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Dutse babban birnin jihar.
Ya ce, an kori dan takarar gwamnan ne saboda sayar da jam’iyyar ga jam’iyyar All Progressives Congress, APC.
Karanta Wannan: Ba mu haɗe da kowacce jam’iyya ba a Kaduna – ADC
Kabiru Hussaini ya bukaci daukacin ‘yan jam’iyyar da su marawa dan takarar gwamna na jam’iyyar PDP, Mustapha Sule Lamido baya.
“Muna umurtar dukkan magoya bayan jam’iyyar mu da su marawa dan takarar gwamna na PDP goyon baya domin PDP ce kadai za ta iya ceto jihar daga rugujewa baki daya,” in ji shi.
Ɗan takarar gwamnan jihar ADC Muhammad Sani Gumel ya janye takararsa ya koma APC.
Da yake mayar da martani, dan takarar gwamna na jam’iyyar ADC Muhammad Sani Gumel, ya ce mukaddashin shugaban jam’iyyar ba shi da hurumin korarsa daga jam’iyyar.
Ya ce hedkwatar kasa ta kori mukaddashin shugaban jam’iyyar ne a ranar 22 ga Satumba, 2022 kuma hukumar INEC, IPAC, da hukumomin tsaro ba su amince da shi ba.