fidelitybank

Mun kashe Ƴan ta’adda uku tare da ƙwato makamai a Kaduna – Sojoji

Date:

Rundunar sojin Najeriya ta ce dakarun runduna ta daya sun kashe ‘yan bindiga uku tare da kwato makamai a Kaduna.

Mukaddashin Daraktan hulda da jama’a na rundunar soji ta daya, Laftanal Kanal Musa Yahaya, ya tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da ya fitar a Kaduna.

“A bisa sahihan bayanan sirri, sojojin runduna ta daya ta sojojin Najeriya da Operation Whirl Punch sun kai wani samame a kusa da dajin Maro – Chibiya a karamar hukumar Kajuru ta jihar Kaduna a ranar 12 ga watan Nuwamba.

“A yayin farmakin, sojoji sun fatattaki ‘yan bindigar da karfin wuta, inda suka kashe daya daga cikin ‘yan bindigar tare da tilasta wa wasu tserewa da harbin bindiga zuwa dajin da ke kewaye,” in ji rundunar.

Rundunar ta kuma ce sojojin sun kama bindiga kirar AK-47 guda daya, bindigar AK-47 na gida guda daya, alburusai 7.62mm (Musamman) hudu da wayar hannu daya.

Yahaya ya kuma bayyana cewa, a ranar 10 ga watan Nuwamba, sojojin runduna da ‘Operation Whirl Punch’ a yayin da suke aikin share fage a kauyukan Kawara da Filin Jalo da ke karamar hukumar Igabi a jihar Kaduna, sun tuntubi ‘yan bindiga a dajin Kawara.

“A fadan da ya barke, sojoji sun kashe dan bindiga guda daya tare da kwato bindiga kirar AK-47 guda daya dauke da alburusai 30 na 7.62mm (Special) da babur daya da wayar fasaha daya yayin da wasu suka tsere da raunukan harbin bindiga,” in ji shi.

spw news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp