fidelitybank

Mun kashe wutar da ta kona ofisoshi 17 a sakatariyar Gwale – Hukumar Kashe Gobara

Date:

Hukumar kashe gobara ta jihar Kano ta tabbatar da afkuwar gobarar da ta tashi a safiyar Laraba da ta kone ofisoshin sakatariyar karamar hukumar Gwale 17.

Jami’in hulda da jama’a na hukumar Saminu Abdullahi ya tabbatarwa da kamfanin dillancin labarai na NAN a Kano faruwar lamarin.

Abdullahi ya ce lamarin ya faru ne da sanyin safiyar Laraba.

“Mun samu kiran waya da misalin karfe 03:43 na safe daga Abdullahi Hassan cewa gobara ta tashi a sakatariyar Gwale.

“Bayan samun labarin, mun aika da motar kashe gobara zuwa wurin da abin ya faru da misalin karfe 03:46 na safe domin shawo kan gobarar,” inji shi.

Abdullahi ya ce benen da aka yi amfani da shi a matsayin ofis mai tsawon mita 300 x 200 da sauransu, wanda ya kai 17, ya lalace gaba daya.

Ya kuma ce an kona motar kirar Peugeot 406, motar Hiace daya da motar daukar marasa lafiya ta tasha.

Ya kuma bada tabbacin hukumar na gudanar da bincike domin gano musabbabin tashin gobarar.

world news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp