fidelitybank

Mun kashe wani jigo na kungiyar IPOB a Imo – Sojoji

Date:

Rundunar soji ta kasa ta ce, dakarunta sun kashe wani mamba na kungiyar IPOB mai fafutukar kafa kasar Biafra a yankin Ihioma da ke karamar hukumar Orlu a jihar Imo.

Wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, Birgediya Janar Onyema Nwachukwu, ya fitar ta ce lamarin ya faru ne a ranar Lahadi.

Ta kara da cewa dakarun nata sun kai farmaki kan mambobin kungiyar, sun kuma yi musayar wuta a wata hanya da ake kira Banana Junction, daya daga cikin yankunan da IOPB ta tilasta wa mutane su rika zaman- gida.

A musayar wutar ce suka yi nasarar kashe kwamandan IPOB din, lamarin da ya sanya sauran suka tsere.

Sojojin dai sun ci gaba da neman wadanda suka tsere da ke ta da zaune-tsaye da hana mazauna yankin sakat.

Sai dai rundunar sojin ta ce IPOB sun fara yada wani bidiyon farfaganda domin jama’a su tausaya musu, inda suka bukaci a yi watsi da shi.

Arangama tsakanin jami’an tsaron Najeriya da mambobin IPOB ba sabon abu ba ne, musamman a yankin kudancin kasar da suke kokarin ballewa da kafa Jamhuriyar Biafra.

legit breaking news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp