fidelitybank

Mun kashe Sarkin ƴan ta’adda da mutane 18 – Sojin Sama

Date:

Shugaban hafsan sojin sama, Air Marshal Oladaya Amao, ya ce, an samu nasarar kashe daya daga cikin sarakunan ‘yan ta’addan, Alhaji Shanono.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa a ranar Alhamis, ta hannun Daraktan hulda da jama’a da yada labarai na rundunar sojin saman Najeriya, Air Commodore Edward Gabkwet.

Ya yi alkawarin cewa, jami’an ba za su huta ba har sai an kawar da ‘yan fashi da ke addabar mutanen da ba su ji ba ba su gani ba a fadin kasar nan.

Babban hafsan sojin ya ba da umarnin a kara kaimi a dukkan sansanin su.

A cewarsa, hare-haren da jiragen saman NAF suka kai a yankin Arewa maso Yamma a baya-bayan nan ya nuna cewa, an kawar da ‘yan ta’adda da dama tare da lalata matsugunan su.

Ya ce, a yayin harin ta sama an kawar da wani sarkin ‘yan ta’adda, Alhaji Shanono da ke aiki a Kaduna tare da wasu ‘yan ta’adda 18, yayin da aka lalata bindigogi sama da 30 da babura 20.

Ya ce, hakazalika, an kai hare-hare ta sama a yankin Arewa maso Gabas tare da taimakon rundunar sojin sama na Operation Hadin Kai, inda suka kai farmaki ta sama kan mayakan ‘yan ta’adda a Gazuwa, jihar Borno a ranar Asabar.

kano news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp