fidelitybank

Mun kashe masu safarar makamai a Gummi zuwa Anka – ‘Yan Sanda

Date:

Bayan sun yi musayar wuta na kusan sa’o’i da masu safarar makaman, waɗanda ake zargin sun ɗauko makaman tun daga jihar Taraba domin kai su sansanin ‘yan ta’adda a Zamfara.

A wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar SP Mohammed Shehu Anipr, ya sanya wa hannu, ya ce lamarin ya faru ne bayan da jami’an nasu suka samu bayanan sirri game da mutanen waɗanda ke cikin ƙaramar mota ƙirar ‘Toyota Corolla’ ɗauke da muggan makamai domin kai su sansanin ‘yan ta’adda a jihar.

Bayan musayar wutar ‘yan sandan sun kama mutum biyu waɗanda suka ji munanan raunuka yayin da wasu suka tsere da raunkan harbi a jikinsu.

An kai mutanen biyu asibiti inda daga baya likita ya tabbatar da cewa sun mutu bayan an kwantar da su a asibitin.

Daga cikin abubuwan da ‘yan sandan suka ƙwato sun haɗar da ƙaramar mota kirar Toyota Corolla, da harsasan manyan bindigogin harba gurneti uku, da abubuwan fashewa uku, da harsasan bindiga ƙirar AK47 151, da harsasan makamin harbo jirgin sama 200, da wasu layu da guraye.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar CP Kolo Yusuf ya sake jadadda burin rundunar na fatattakar ‘yan bindiga da sauran masu aikata miyagun laifuka daga jihar, domin tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a faɗin jihar.

legit.ng.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An gargadi al’umma su yi taka tsan-tsan da ambaliyar ruwan sama

Yayin da ake ci gaba da fuskantar saukar ruwan...

Gwamnatin Tarayya za ta gina hanyar sufurin jirgin ƙasa a Kano

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta samar da titin...

Abin da ya sa muke ci gaba da tsare Sowore – Ƴansanda

Kwamishinan ƴansanda mai kula da sashen kai ɗauki na...

INEC za ta bai wa ɗaurarru damar kaɗa ƙuri’a a lokacin zaɓuka

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta ta duba yiwuwar bai...

Mai ya jawo Matan Zamfara su ka yi zanga-zanga

Ɗaruruwan mata ne tsofaffi da masu shawarya suka gudanar...

Aƙalla mutane 24,000 ne suka ɓata saboda Boko Haram a Najeriya

Kungiyar Agaji ta Red Cross ta bayyana cewa aƙalla...

‘Yansanda ku gaggauta sakin Sowore – Obi

Tsohon ɗan takarar shugaban kasa a jam'iyyar LP, Peter...

PDP ta gargaɗi mambobinta kan goyon bayan Tinubu

Babbar jam'iyyar hamayya ta PDP a Najeriya ta gargaɗi...

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...
X whatsapp