Hedkwatar tsaro ta ƙasa, ta ce, dakarun soji sun hallaka ‘yan ta’adda 191, tare da kubutar da fararen hula 91 da aka sace.
Haka kuma dakarun soji sun kama wadanda suka kira ‘yan ta’adda 206 da masu satar man fetur da kuma masu garkuwa da mutane. Sun kuma ce mayakan Boko Haram da iyalansu 104 ne suka mika wuya ga sojojin Najeriya a yankin arewa maso gabas.
Daraktan yada labaran tsaro, Manjo Janar Edward Buba who made this known on Thursday stated that troops equally denied oil theft perpetrators, the stealing of crude oil products estimated at the sum of N388,46million.
“Sojoji sun gano tare da lalata hramattun wajen haƙo mai 34, da rijiyoyin da ake tara man 38, jirage 21 da tankunnan mai 57 da tiyon zuƙo mai 3, sai na’urar gashi ta girki 89 a Neja Delta. sojojin sun kuma ƙwato litar ɗanyen mai 696,250 da aka sace da litar mai da aka haƙo ba bisa ƙa’ida ba 54,400 da kuma tattaccen fetur 1,200.”