fidelitybank

Mun kara yawan ma’aikatan lafiya dubu 64 daga 28 a makarantun lafiya – Ministan Lafiya

Date:

Ministan lafiya da walwalar jama’a, Farfesa Muhammad Pate a ranar Juma’a ya ce, an kara yawan adadin masu rajista a makarantun likitanci, aikin jinya da sauran makarantun kwararrun lafiya daga 28,000 zuwa 64,000 duk shekara.

Farfesa Pate ya bayyana haka ne a wajen taron manema labarai na bangaren ministoci na bikin cikar shugaban kasa Bola Tinubu a kan karagar mulki a Abuja.

“Wannan shi ne mataki na farko, bangaren ilimi zai taka rawar gani. Jihohin za su taka rawa wajen inganta ababen more rayuwa, horarwa, da kayan aikin da za su samar da karin ma’aikatan kiwon lafiya saboda muna bukatar samar da karin ma’aikatan kiwon lafiya ganin cewa muna asarar wasu domin mu yi wa al’ummar kasar nan hidima.”

Akan cibiyoyin kula da lafiya a matakin farko, ministar ta lura cewa aƙalla cibiyoyi 1,400 ne za su iya ba da ƙwararrun ma’aikatan haihuwa.

A cewarsa, sama da ma’aikatan lafiya 2,400 – likitoci, ma’aikatan jinya, da ungozoma ake daukar aiki a wuraren da za su samar da muhimman ayyukan kiwon lafiya ga ‘yan Najeriya a yankunan karkara.

Ya kuma kara da cewa gwamnatin tarayya ta biya kason farko na N25bn na asusun kula da lafiya na asali ta hannun hukumar kula da lafiya matakin farko ta kasa da kuma hukumar inshorar lafiya ta kasa.

“Mun sanya sharadin cewa jihohin da za su shiga wadanda dole ne su bi ka’idojin amintattu da aka tanada, tare da mayar da martani ga kura-kurai da aka lura a nan domin albarkatun su tafi ga ‘yan Najeriya.

“Jihohi 23 ne suka karbi wadannan kudade, kuma na yi imanin cewa sauran jihohin sun kusa kammalawa da karbar kudaden su ta hanyar PHCs.”

nigeria news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp