A ranar Lahadi ne hukumar alhazai ta kasa NAHCON ta kammala jigilar maniyyata aikin hajjin shekarar 2022 zuwa gida.
Jirgin karshe na aikin hajjin 2022, jirgin Azman Air mai alhazai 319 daga Kaduna da Kano da jamiāan jihohi daban-daban da NAHCON ya tashi daga filin jirgin sama na Sarki Abdul Aziz a Jidda, ranar 7 ga watan Agusta da misalin karfe 12:00 na rana.
Tafiyar ta nuna karshen ayyukan Hajji na 2022 daga Najeriya.
Kimanin alhazan Najeriya 43,008 ne suka gudanar da aikin hajji a kasar Saudiyya.
Jamiāar hulda da jamaāa na hukumar Fatima Usara a cikin wata sanarwa da ta fitar, ta ce jirgin na karshe na zuwa ne kwanaki shida gabanin waāadin aikin Hajji kamar yadda hukumomin Saudiyya suka kayyade, kuma kwanaki uku gabanin waāadin hukumar NAHCON ya kasance 10 ga Agusta, 2022. .
A cewarta, sama da makonni uku ana gudanar da aikin, an soke tashin jirage biyu ne kawai tare da tsaikon da ya kai na sa’o’i shida.