Dakarun ‘yan sandan Jihar Zamfara, sun kashe ɗan fashin daji tare da kama wasu shida da ake zargi da fashin da kuma satar shanu, a cewarta.
Da yake gabatar da waɗanda ake zargin a ranar Laraba, kakakin ‘yan sanda SP Mohammed Shehu ya ce dakarun sun ƙwace bindiga ƙirar AK-47 biyu, da fakitin harsasai biyu, da tarin layu, da sauransu.
A cewarsa: “A ranar 1 ga watan Janairun 2023, rundunar ta samu wani rahoton gaggawa kan ‘yan fashin daji a yankin Gusau-Magami-Dansadau. ‘Yan sanda sun isa wurin kuma suka far wa ‘yan bindigar.
“Cikin sa’a, an kashe ɗaya daga cikinsu kuma aka daƙile harinsu, suka gudu daji da raunukan bindiga.”
Haka nan, ‘yan sandan sun yi nasarar kama wani da ke da alaƙa da jagoran ‘yan fashi Halilu Kacalla mai suna Musbahu Aminu.
SP Shehu ya ce matashin mai shekara 30 ya amsa laifin aikata fashi da makami da satar shanu masu yawa a yankin.