fidelitybank

Mun kama ‘yan fashin Daji 6 a Zamfara ‘Yan Sanda

Date:

Dakarun ‘yan sandan Jihar Zamfara, sun kashe ɗan fashin daji tare da kama wasu shida da ake zargi da fashin da kuma satar shanu, a cewarta.

Da yake gabatar da waɗanda ake zargin a ranar Laraba, kakakin ‘yan sanda SP Mohammed Shehu ya ce dakarun sun ƙwace bindiga ƙirar AK-47 biyu, da fakitin harsasai biyu, da tarin layu, da sauransu.

A cewarsa: “A ranar 1 ga watan Janairun 2023, rundunar ta samu wani rahoton gaggawa kan ‘yan fashin daji a yankin Gusau-Magami-Dansadau. ‘Yan sanda sun isa wurin kuma suka far wa ‘yan bindigar.

“Cikin sa’a, an kashe ɗaya daga cikinsu kuma aka daƙile harinsu, suka gudu daji da raunukan bindiga.”

Haka nan, ‘yan sandan sun yi nasarar kama wani da ke da alaƙa da jagoran ‘yan fashi Halilu Kacalla mai suna Musbahu Aminu.

SP Shehu ya ce matashin mai shekara 30 ya amsa laifin aikata fashi da makami da satar shanu masu yawa a yankin.

taraba state today news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

INEC za ta bai wa ɗaurarru damar kaɗa ƙuri’a a lokacin zaɓuka

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta ta duba yiwuwar bai...

Mai ya jawo Matan Zamfara su ka yi zanga-zanga

Ɗaruruwan mata ne tsofaffi da masu shawarya suka gudanar...

Aƙalla mutane 24,000 ne suka ɓata saboda Boko Haram a Najeriya

Kungiyar Agaji ta Red Cross ta bayyana cewa aƙalla...

‘Yansanda ku gaggauta sakin Sowore – Obi

Tsohon ɗan takarar shugaban kasa a jam'iyyar LP, Peter...

PDP ta gargaɗi mambobinta kan goyon bayan Tinubu

Babbar jam'iyyar hamayya ta PDP a Najeriya ta gargaɗi...

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...

Mukarraban gwamnati ba zan lamunci dabi’ar zubar da kima ta ba – Abba

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya gargaɗi masu...

WAEC ta sake bude shafinta don duba jarabawar bana

Hukumar shirya jarabawar Afirka ta Yamma (WAEC) ta bayyana...

Indonesia za ta gina asibiti dubu biyu ga Falasɗinawa

Indonesia ta sanar da cewa za ta kafa wata...
X whatsapp