fidelitybank

Mun kama wanda ya damfari abokin sa a Jigawa – NSCDC

Date:

Hukumar tsarota ta NSCDC, ta kama wani matashi dan shekara 30 mai suna Shamsu Haruna da laifin damfarar abokansa a karamar hukumar Jahun ta jihar Jigawa.

Kakakin hukumar NSCDC CSC Adamu Shehu ya bayyana haka a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a ranar Juma’a.

Ya ce an kama wanda ake zargin ne biyo bayan korafin da wani Abdussalam Ya’u da wasu mutane biyu suka shigar na cewa wanda ake zargin ya hada baki da wasu mutane tare da damfarar su Naira miliyan 2,816,500 domin samar musu da kayayyakin noma da taki a farashi mai rahusa.

Adam ya ce daga baya wadanda abin ya shafa suka gane yaudara ce, kuma duk kokarin da aka yi na kwato kudadensu ya ci tura, wanda hakan ya sa suka kai rahoton lamarin ga NSCDC a Jahun.

Ya ce wanda ake zargin ya amsa laifin aikata laifin tare da bayyana sunayen wasu mutane hudu da suka hada da Oga Muhammad, Oga Abdullahi, Abdurrahman, da Yusuf Hadejia, wadanda yanzu haka suke gudu a matsayin wadanda suka taimaka masa.

Ya bayyana cewa ana tuhumar wadanda ake zargin ne da laifin hada baki da kuma zamba da ya saba wa sashi na 96 da 320 da kuma hukuncin da ya dace a karkashin sashe na 97 da 322 na dokar penal code na jihar Jigawa CAP P3 VOL. III Dokokin Jihar Jigawa 2012.

Adam ya ce rundunar tana kokarin cafke sauran mutane hudun da ake zargi domin gurfanar da su gaban kotu.

punch newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...
X whatsapp