fidelitybank

Mun kama wanda ya damfari abokin sa a Jigawa – NSCDC

Date:

Hukumar tsarota ta NSCDC, ta kama wani matashi dan shekara 30 mai suna Shamsu Haruna da laifin damfarar abokansa a karamar hukumar Jahun ta jihar Jigawa.

Kakakin hukumar NSCDC CSC Adamu Shehu ya bayyana haka a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a ranar Juma’a.

Ya ce an kama wanda ake zargin ne biyo bayan korafin da wani Abdussalam Ya’u da wasu mutane biyu suka shigar na cewa wanda ake zargin ya hada baki da wasu mutane tare da damfarar su Naira miliyan 2,816,500 domin samar musu da kayayyakin noma da taki a farashi mai rahusa.

Adam ya ce daga baya wadanda abin ya shafa suka gane yaudara ce, kuma duk kokarin da aka yi na kwato kudadensu ya ci tura, wanda hakan ya sa suka kai rahoton lamarin ga NSCDC a Jahun.

Ya ce wanda ake zargin ya amsa laifin aikata laifin tare da bayyana sunayen wasu mutane hudu da suka hada da Oga Muhammad, Oga Abdullahi, Abdurrahman, da Yusuf Hadejia, wadanda yanzu haka suke gudu a matsayin wadanda suka taimaka masa.

Ya bayyana cewa ana tuhumar wadanda ake zargin ne da laifin hada baki da kuma zamba da ya saba wa sashi na 96 da 320 da kuma hukuncin da ya dace a karkashin sashe na 97 da 322 na dokar penal code na jihar Jigawa CAP P3 VOL. III Dokokin Jihar Jigawa 2012.

Adam ya ce rundunar tana kokarin cafke sauran mutane hudun da ake zargi domin gurfanar da su gaban kotu.

www.nnn.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Barrister Sa’idu ya kama aiki bayan ya maye gurbin Muhyi Magaji

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya rantsar...

An ceto Mutane 26 da kwale-kwale ya kife da su a Sokoto

An samu nasarar ceto mutum 29 bayan hatsarin kwale-kwale...

An ceto Mutane 26 da kwale-kwale ya kife da su a Sokoto

An samu nasarar ceto mutum 29 bayan hatsarin kwale-kwale...

Barau zai mayar da filin wasan BUK na zamani

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya...

Jami’ar Bayero ta Kano ta yi sabon shugaba

Farfesa Haruna Musa, ya karɓi ragamar shugabancin jami’ar Bayero...

Gwamnatin Kano ta amince Barau FC ta yi wasa a filin Sani Abacha

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da kungiyar kwallon kafa...

Gwamnatin Tinubu na takalar Kwankwaso da fada – Buba Galadima

Jigo a jam'iyyar NNPP, kuma na hannun tsohon gwamnan...

Newcastle United ta dauki dan wasan tsakiya Jacob daga Aston Villa

Newcastle United ta sanar da daukar dan wasan tsakiya...

Hisba ta kama ‘yan Mata 62 da zargin aikata baɗala a Kano

Hukumar Hisbah ta kama mutane 62 kan zargin aikata...

NNPP ta yi tafka magudi a zabencike gurbin Kano – Farouk Lawan

Tsohon dan majalisar wakilai, Farouk Lawan, ya yi zargin...

Dan shugaban kungiyar Boko Haram ya shiga hannu

Hukumomi a ƙasar Chadi sun kama yaron shugaban ƙungiyar...
X whatsapp