Rundunar sojin ruwan Najeriya da ke yaki da masu satar ɗanyen mai, sun ce sun kama tare da lalata tataccen litar gas 15,775 a yankin Igbokoda na ƙaramar hukumar Ilaje da ke jihar Ondo a kudancin ƙasar.
Rahotanni na cewa, sojojin sun yi kaman ne a ranar Lahadi, inda suka lalata man da suka ce zai kai na miliyoyin naira.
Babban jami’in tawagar sojojin, Commander Humphrey Nnaji ne ya bayyana haka ranar Lahadi.
Ya ce jami’an sojin sun samu bayanan sirri kan masu aikata laifin kafin su kai samamen.
Ya ƙara da cewa rundunar ta kuma samu nasarar ƙwato man da ake tacewa, tare da ƙwato wani kwale-kwale da ɗanyen mai a cikinsa.