fidelitybank

Mun kama sojojin Koriya ta Arewa a Rasha – Ukraine

Date:

Shugaban ƙasar Ukraine Volodymyr Zelensky ya bayyana cewa, sojojin ƙasar Ukraine sun kama wasu sojojin Koriya ta arewa biyu da suka jikkata a matsayin fursunonin yaki a yankin Kursk na ƙasar Rasha.

Mutanen biyu suna samun kula a asibiti kuma suna hannun Hukumar Tsaro ta Ukraine (SBU) a birin Kyiv, a cewar Zelensky.

Shugaban ya ce yana godiya ga sojojin Ukraine da dakarun soji na musamman da suka kama ƴan Koriya ta Arewan.

Ya ƙara da cewa “wannan ba abu ne mai sauki ba”, yana mai cewa sojojin Rasha da Koriya ta Arewa sukan kashe ƴan Koriya ta Arewa da suka samu raunuka “don shafe duk wata shaida da ke nuna cewa Koriya ta Arewa na da hannu a yaƙin da ake yi da Ukraine”.

“Duniya na buƙatar sanin gaskiya game da abin da ke faruwa.” in ji Zelensky

Zelensky ya kuma wallafa hotunan wasu mutane biyu da suka jikkata amma bai bayar da shaidar cewa su Koriya ta Arewa ba ne.

vanguard news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp