fidelitybank

Mun kama mutane biyu da suke lalata layin dogo – NSCDC

Date:

Hukumar tsaro ta NSCDC, ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da lalata layukan dogo a jihar Enugu.

Mista Aloysius Obiorah, Kwamandan NSCDC a jihar, ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Laraba a Enugu ta hannun Mista Denny Manuel, jami’in hulda da jama’a na rundunar.

Obiorah ya ce, wadanda ake zargin, Onu Chekwube, mai shekaru 28, da Okeke Okwudiri, mai shekaru 18, an kama su ne a ranar 10 ga Oktoba a kauyen Aruokwe, Oduma a karamar hukumar Aninri ta jihar.

Ya ce an kama su ne a lokacin da suke tarwatsa ayyukan layin dogo mallakin kamfanin jiragen kasa na Najeriya.

Kwamandan ya ce an kwato bololin jirgin kasa guda 77 da na goro, bututun ƙarfe, diger da adduna, rig spanner, fanfunan ruwa na hydraulic acid, flat spanner da cikakkun kwantena biyu na na’urar ruwa daga hannun waɗanda ake zargin.

Ya ce an kama mutanen biyu ne tare da goyon bayan mafarauta da wasu ma’aikatan hukumar tsaron dajin jihar.

Obiorah ya bukaci al’ummar jihar da su taimaka wa jami’an tsaro da bayanai kan ayyukan masu aikata laifuka domin daukar matakin gaggawa.

Kwamandan NSCDC ya jaddada cewa bayanan sirri na al’umma na da mahimmanci don dakile ayyukan aikata laifuka a kan lokaci.

Ya ce za a gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kotu bayan cikakken bincike. (NAN)

thisdaynews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp