Hukumar tsaro ta NSCDC, reshen jihar Kano, ta ce, ta kama mutane akalla 93 da ake zargi da aikata laifuka daban-daban a jihar tsakanin watan Janairu zuwa Maris.
Adamu Salihu, Kwamandan NSCDC na jihar ne ya bayyana hakan a wata hira da kamfanin dillancin labarai na (NAN) a Kano ranar Juma’a.
Salihu ya ce an kama wadanda ake zargin ne da laifin sata, barna da cin amana da sauransu.
“Daga cikin wadanda ake tuhuma 93, 29 an gurfanar da su a gaban kotu, 57 da ake tuhuma suna kan bincike kuma mun samu hukunci guda bakwai a cikin wannan lokaci,” inji shi.
Kwamandan ya nanata kudurin NSCDC na karewa da kuma kiyaye duk wasu muhimman kadarori da ababen more rayuwa na kasa.
Ya kuma bukaci jama’a da su tallafa wa jami’an tsaro da bayanan tsaro masu amfani domin tabbatar da zaman lafiya a jihar, ya kara da cewa tsaro ya zama alhakin kowane dan kasa.