Akalla mutane 793 ne jami’an hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA, suka kama a babban birnin tarayya Abuja a shekarar da ta gabata.
Kwamandan NDLEA a babban birnin tarayya, Kabir Tsakuwa, a lokacin da yake zantawa da manema labarai yayin wani gangamin wayar da kan jama’a game da illolin miyagun kwayoyi a ranar Talata, ya kuma tabbatar da cewa hukumar ta NDLEA ta kama miyagun kwayoyi 13,125kg a babban birnin kasar nan.
Dr Ngozi Madubuike, Daraktar Rage Bukatun Magunguna, NDLEA ce ta jagoranci wayar da kan jama’a.
Karanta Wannan: NDLEA ta gana da hukumomin Pakistan a kan dakile safarar kwayoyi
A cewarsa, a cikin shekarar da ta gabata, an kama 13,125kg na wasu abubuwa daban-daban na miyagun kwayoyi, inda ya ce fasa-kwaurin magungunan da aka kama sun hada da kilogiram 12,660.3 na tabar wiwi sativa.
Sauran, in ji shi, sun hada da 21.957kg na hodar iblis, 0.008kg na tabar heroin da 443.693kg na abubuwa daban-daban na psychotropic.
An yi nasarar yi wa mutane saba’in da takwas, wadanda suka hada da maza 74 da mata hudu masu fama da matsalar shan miyagun kwayoyi shawara tare da gyara su a cikin lokaci guda.
Ya ce, “Shirye-shiryen namu na ba da shawara da kuma gyara sun ba da sakamako mai kyau a yankin. A halin da ake ciki, a cikin wannan lokaci, an kama jimillar mutane 793 da suka hada da maza 768 da mata 29, kuma an yanke musu hukunci 167, wadanda 161 maza ne, mata shida.”