fidelitybank

Mun kama mutane 793 a Abuja – NDLEA

Date:

Akalla mutane 793 ne jami’an hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA, suka kama a babban birnin tarayya Abuja a shekarar da ta gabata.

Kwamandan NDLEA a babban birnin tarayya, Kabir Tsakuwa, a lokacin da yake zantawa da manema labarai yayin wani gangamin wayar da kan jama’a game da illolin miyagun kwayoyi a ranar Talata, ya kuma tabbatar da cewa hukumar ta NDLEA ta kama miyagun kwayoyi 13,125kg a babban birnin kasar nan.

Dr Ngozi Madubuike, Daraktar Rage Bukatun Magunguna, NDLEA ce ta jagoranci wayar da kan jama’a.

Karanta Wannan: NDLEA ta gana da hukumomin Pakistan a kan dakile safarar kwayoyi

A cewarsa, a cikin shekarar da ta gabata, an kama 13,125kg na wasu abubuwa daban-daban na miyagun kwayoyi, inda ya ce fasa-kwaurin magungunan da aka kama sun hada da kilogiram 12,660.3 na tabar wiwi sativa.

Sauran, in ji shi, sun hada da 21.957kg na hodar iblis, 0.008kg na tabar heroin da 443.693kg na abubuwa daban-daban na psychotropic.

An yi nasarar yi wa mutane saba’in da takwas, wadanda suka hada da maza 74 da mata hudu masu fama da matsalar shan miyagun kwayoyi shawara tare da gyara su a cikin lokaci guda.

Ya ce, “Shirye-shiryen namu na ba da shawara da kuma gyara sun ba da sakamako mai kyau a yankin. A halin da ake ciki, a cikin wannan lokaci, an kama jimillar mutane 793 da suka hada da maza 768 da mata 29, kuma an yanke musu hukunci 167, wadanda 161 maza ne, mata shida.”

www.legitnews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp