fidelitybank

Mun kama mutane 793 a Abuja – NDLEA

Date:

Akalla mutane 793 ne jami’an hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA, suka kama a babban birnin tarayya Abuja a shekarar da ta gabata.

Kwamandan NDLEA a babban birnin tarayya, Kabir Tsakuwa, a lokacin da yake zantawa da manema labarai yayin wani gangamin wayar da kan jama’a game da illolin miyagun kwayoyi a ranar Talata, ya kuma tabbatar da cewa hukumar ta NDLEA ta kama miyagun kwayoyi 13,125kg a babban birnin kasar nan.

Dr Ngozi Madubuike, Daraktar Rage Bukatun Magunguna, NDLEA ce ta jagoranci wayar da kan jama’a.

Karanta Wannan: NDLEA ta gana da hukumomin Pakistan a kan dakile safarar kwayoyi

A cewarsa, a cikin shekarar da ta gabata, an kama 13,125kg na wasu abubuwa daban-daban na miyagun kwayoyi, inda ya ce fasa-kwaurin magungunan da aka kama sun hada da kilogiram 12,660.3 na tabar wiwi sativa.

Sauran, in ji shi, sun hada da 21.957kg na hodar iblis, 0.008kg na tabar heroin da 443.693kg na abubuwa daban-daban na psychotropic.

An yi nasarar yi wa mutane saba’in da takwas, wadanda suka hada da maza 74 da mata hudu masu fama da matsalar shan miyagun kwayoyi shawara tare da gyara su a cikin lokaci guda.

Ya ce, “Shirye-shiryen namu na ba da shawara da kuma gyara sun ba da sakamako mai kyau a yankin. A halin da ake ciki, a cikin wannan lokaci, an kama jimillar mutane 793 da suka hada da maza 768 da mata 29, kuma an yanke musu hukunci 167, wadanda 161 maza ne, mata shida.”

nhgsfp

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...

A shirye nake na mutu don nasarar APC a 2027 – Orji Kalu

Sanatan Abia ta Arewa, Orji Uzor Kalu, ya bayyana...

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...
X whatsapp