fidelitybank

Mun kama mutane 15 mun kwace motoci 20 a Kano – ‘Yan Sanda

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta ce, ta kama mutane 15 tare da kwato motoci 20 da aka sace a sassan jihar.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan, SP Abdullahi Kiyawa ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Talata a Kano.

Ya ce kamawa tare da kwato motocin da aka sace ya samo asali ne daga kudurin rundunar na kawo karshen duk wasu laifuka a jihar.

Kiyawa ya ce, “Mun himmatu sosai wajen yakar satar motoci da duk wani nau’in aika aika a wuraren da muke sa ido.

“A cikin watan da ya gabata, rundunar ‘yan sandan ta ci gaba da nuna jajircewar ta na tabbatar da kare rayuka da dukiyoyin daukacin mazauna jihar.

“Wannan yana ci gaba da bin umarni da hangen nesa na I-G Egbetokun ga duk umarnin ‘yan sanda da tsare-tsare don aiwatar da aikin ‘yan sanda na al’umma, aikin ‘yan sanda da bayanan sirri, da nuna kwarewar kwararru don isar da sabis mai inganci.”

Da yake godiya ga jama’a bisa fahimtarsu, hadin kai, da goyon bayansu, kwamishinan ‘yan sanda, Usaini Gumel, ya jaddada aniyar rundunar na yin aiki cikin doka.

Ya kuma shawarci kowa da kowa da ya ci gaba da kai rahoton duk wani motsi ko mutum ko wani abu da ake zargi ga ofishin ‘yan sanda na yankin domin daukar matakin tsaro cikin gaggawa.

daily sun news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp