Shugaban hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa (NDLEA) Buba Marwa, ya tabbatar da cewa, hukumar ta kama mutane 11,340 da a ke zargi da safarar miyagun kwayoyi tare da hukunta mutane 1,111 a cikin watanni 11.
Marwa ya bayyana haka ne a Abuja a wani taro da Daraktoci da Kwamandojin Shiyya da na Kwamandojin Jiha da na Musamman, a ranar Talata.
A cewar Marwa,”Adadin wadanda a ka kama da kuma hukuncin da hukumar ta kama ya karu. Alkaluman ayyukan rage samar da magunguna sun karu, an kama mutane 11, 340 tare da hukunta mutane 1,111 a cikin watanni 11,” inji shi.
“A cikin watanni 11, mun yi nasarar kwashe fiye da kilogiram 3.3 na magunguna iri-iri; nesa da titunan Najeriya; nesantar masu laifi, ‘yan ta’adda da ‘yan fashi; nesa da matasan mu.
“Wannan bikin karramawa da yabo ya shaida cewa shugabancin hukumar ta NDLEA na ci gaba da bin diddigin sa, domin zaburar da ma’aikatan NDLEA a matsayin hanyar fitar da hukumar daga kangin da ta yi fama da shi tsawon shekaru”. A cewar Marwa.
Shugaban ya kuma bukaci jami’an hukumar da su yi wa barayin miyagun kwayoyi da masu fataucin miyagun kwayoyi wahala a shekarar 2022.
Ya kuma yabawa shugaban kasa Muhammadu Buhari bisa goyon baya da kwarin gwiwa da ya ke baiwa hukumar ta NDLEA da ayyukanta.
A wajen taron an baiwa wasu kwamandojin jihohi hudu da jami’ai 25 lambar yabo na kudi da kuma wasikun yabo bisa ga kwazon da suka nuna.