Rundunar ‘yan sandan jihar Oyo ta tabbatar da cewa, wani dan sanda ya harbe wani dalibi har lahira.
A wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, Adewale Osifeso, ya fitar, kwamishinan ‘yan sandan, CP Ngozi Onadeko, ya bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike kan mutuwar wanda aka kashe, Samuel Akinsuyi, a kan hanyar Eruwa zuwa Ibadan a ranar Juma’a 11/03/2022. .
Ya ce, an gano jami’an da abin ya shafa, an kama su, tare da gudanar da bincike a kan su.
Domin haka kwamishinan ‘yan sandan ya bukaci a kwantar da hankula tare da ba da tabbacin gudanar da cikakken bincike, domin gano abubuwan da suka haddasa faruwar lamarin.