fidelitybank

Mun kama budurwa da ta binne jariri a banɗaki – Ƴan Sandan Jigawa

Date:

Rundunar ‘yan sanda ta jihar Jigawa, ta ce, jami’anta sun kama wata mata mai suna Balaraba Shehu da ke ƙauyen Tsurma a ƙaramar hukumar Kiyawa, bisa zargin binne sabon jaririn da ta haifa a ban ɗaki.

Yayin da yake tabbatar wa da BBC faruwar lamarin, mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar DSP Lawan Shiisu Adam ya ce, sakamakon bayanan sirrin da rundunarsu ta samu ne ya kai su ga gano matar tare da tono jaririn a ban ɗakin gidan.

”Bayan haihuwar ta ne sai ta shiga ban ɗaki ta haƙa rami a kusa da masai ta binne jaririn”

Ya ce, bayan tono jaririn ne aka garzaya da shi babban asibitin Dutse inda likitoci suka tabbatar da cewa ya rasu.

DSP Shiisu Adam ya ce, matar ta sanar da su cewa ta samu cikin ne ba ta hanyar aure ba, ta kuma bayyana wani saurayinta mai suna Ahmadu Sale wanda aka fi sani da ‘Dan kwairo’ da ta ce shi ne ya yi mata cikin.

Kawo yanzu dai matar mai shekara 30 tare da saurayin nata mai shekara 25 suna hannun jami’an ‘yan sanda.

Tuni kwamishinan ‘yan sandan jihar ya bayar da umarnin mayar da batun zuwa shalkwatar cibiyar binciken manyan laifuka ta rundunar da ke babban birnin jihar Dutse.

current eggon news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...
X whatsapp