fidelitybank

Mun kama ƴan Daba masu ƙwacen waya 98 a Kaduna – Gwamnati

Date:

Gwamnatin jihar Kaduna ta tabbatar da kama ‘yan daba da masu ƙwacen wayoyi da aka fi sani da ‘yan ‘Sara-Suka’ 98 a jihar.

Gwamnan jihar Mallam Nasir El-Rufai ne ya buƙaci ɗaukar tsattsauran mataki kan ɓata-garin, sakamakon ƙaruwar ayyukan ‘yan daba da masu ƙwacen wayoyi a ƙwaryar birnin Kaduna.

Cikin wata sanarwa da kwamishinan tsaro da al’amuran cikin gida na jihar Samuel Aruwan ya fitar ya ce an gurfanar da 19 daga cikinsu a gabon kotu, yayin da ake ci gaba da bincike kan mutane 61, kafin a gurfanar da su.

Ɓata-garin kan farmaki mutane tare da ƙwace musu wayoyi da sauran kayayyaki, lamarin da ya yi sanadiyyar rasa rayuka tare da jikkata mutane masu yawa.

Rahoton kamen wanda ‘yan sanda suka fitar, ya ce an kama ‘yan dabar a ranakun 26 da 28 ga watan Afrilu.

Rahoton ya ce 18 daga cikin ɓata-garin an kai su sashen binciken manyan laifuka na rundunar ‘yan sandan jihar domin faɗaɗa bincike, gabanin gurfanar da su a gaban kotu.

Gwamnan jihar ya umarci rundunar ‘yan sandan da su tabbatar da yin abin da ya dace domin gurfanar da su a gaban kotu, tare da faɗaɗa bincike don kamo duk masu aikata irin wannan ta’asa a faɗin jihar.

El-Rufai ya kuma jajanta wa iyalan waɗanda suka rasa rayukansu, tare da fatan samun sauƙi ga waɗanda suka jikkata, sanadiyyar ayyukan ‘yan bindigar.

Daga ƙarshe gwamnan ya yi kira ga al’umma musamman mazauna unguwannin da ake wannan ta’asa da su kai sunayen ‘yan dabar da ke addabar yankunansu ga jami’an tsaro domin a bibiye su

legitnewsnigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp