fidelitybank

Mun kafa kwamitin da zai duba hare-haren da muka kai kan fararen hula – Sojoji

Date:

Babban Hafsan Sojan Sama na kasa, Air Marshal Oladayo Amoa, ya ce, rundunar ta kafa wani kwamiti da zai tattaro bayanai kan dukkan lamuran kai hari bisa kuskure kan fararen hula da sojojin saman kasar suka yi.

A cewarsa kwamitin wanda ya kunshi manyan jami’an rundunar zai yi bitar abubuwan da suka faru har aka kai ga faruwar hakan domin daukar matakan magance su.

A cewar wata sanarwa da rundunar ta fitar, Air Marshal Amao ya sanar da hakan ne a yau Alhamis, yayin da yake bude taron karawa-juna-sani kan aikace-aikacen rundunar sojin saman na shekara ta 2022 da ke gudana yanzu haka a Uyo, babban birnin jihar Akwa-Ibom.

A cewarsa manufar hakan ita ce samun shawarwari kan muhimman matakan da ya kamata a dauka domin rage yawan kashewa da raunata fararen hula a kasar yayin wasu aikace-aikacen da rundunar ta sojin sama ke yi a wasu sannan kasar.

Air Marshal Amao ya kuma kara da cewa binciken yana kuma da manufar kara tabbatar ana bin Kadin yadda sojojin rundunar ke aiwatar da umarnin da aka ba su da ba rundunar ta NAF damar koyon wasu muhimman darussan kan yadda za ta kaucewa faruwar hakan a gaba ko kuma rage irin ta’adin da irin wannan kuskure ke yi.

Kazalika da kuma daukar karin matakai don rage cutar da fararen da ke zaune a yankunan da ke fama da tashe-tashen hankula.

Yayin da yake taya sabbin matasan matukan jiragen yaʙi 17 da aka yaye a wajen taron, Mista Amao ya hore da su bi ka’idojin aiki da aka shimfida a yayin da suke fagen daga, kana su dauki dukkan matakan da suka wajaba wajen kare fararen hula da kuma rage illata su.

Sai dai sanarwar, wadda mai magana da yawun rundunar Air Commodore Edward Gabkwet ya fitar ba ta sanar da lokacin da ake tsammanin kammala wannan binciken da fitar da sakamako ba.

Mutuwa da kuma raunata fararen-hula a cikin hare-haren sojojin sama a Najeriya abu ne da ke ta maimaituwa a shekarun bayan bayan nan, tun bayan sakin wani bam bisa kuskure da suka yi a garin Rann na jihar Borno wannan ya yi sanadin mutuwar ā€˜yan gudun hijira da ma’aikatan agaji fiye da dari daya shekaru biyar da suka wuce.

Ko a watan Satumban bara ma fararen hula fiye da 10 ne suka rasa rayukansu a kauyen Buhari na jihar Yobe wasu kuma 20 suka samu raunuka a wani harin da wani jirgin saman soji ya kai musu bisa kuskure.

Lamarin dai bai tsaya kan fararen hula ba kadai domin wasu sojoji da dama sun rasa rayukansu a wata Afrilun barar lokacin da wani jirgin yaʙi ya kai wa motar su hari bisa kuskure a yankin Mainok na jihar Borno bayan da sojojin na kasa suka kira a kawo musu dauki a arangamar da suke yi da mayakan Boko Haram a lokacin.

Akwai lamurra makamantan haka da suka faru a wasu yankuna cikin har da jihar Zamfara inda sojojin ke fada da ā€˜yan fashin daji.

nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Hisbah za ta yi wa ‘yan Daban Kano aure

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta sanar da wani...

Ganduje ya dawo Najeriya bayan ya shafe wata guda a Landan

Tsohon shugaban jam’iyyar APC na ʙasa, Dr. Abdullahi Ganduje,...

Barrister Sa’idu ya kama aiki bayan ya maye gurbin Muhyi Magaji

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya rantsar...

An ceto Mutane 26 da kwale-kwale ya kife da su a Sokoto

An samu nasarar ceto mutum 29 bayan hatsarin kwale-kwale...

An ceto Mutane 26 da kwale-kwale ya kife da su a Sokoto

An samu nasarar ceto mutum 29 bayan hatsarin kwale-kwale...

Barau zai mayar da filin wasan BUK na zamani

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya...

Za mu ladabtar da Jami’an mu da aka gansu suna taimakawa ‘yan siyasa a Kano – ‘Yansanda

Rundunar ʓan sanda ta jihar Kano ta ce, ta...

Jami’ar Bayero ta Kano ta yi sabon shugaba

Farfesa Haruna Musa, ya karɓi ragamar shugabancin jami’ar Bayero...

Gwamnatin Kano ta amince Barau FC ta yi wasa a filin Sani Abacha

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da kungiyar kwallon kafa...

Gwamnatin Tinubu na takalar Kwankwaso da fada – Buba Galadima

Jigo a jam'iyyar NNPP, kuma na hannun tsohon gwamnan...

Newcastle United ta dauki dan wasan tsakiya Jacob daga Aston Villa

Newcastle United ta sanar da daukar dan wasan tsakiya...

Hisba ta kama ‘yan Mata 62 da zargin aikata baɗala a Kano

Hukumar Hisbah ta kama mutane 62 kan zargin aikata...
X whatsapp