fidelitybank

Mun jinjina wa abokan hamayya da suka kai mu kotu – APC

Date:

Jam`iyyar APC ta ce nasarar da Bola Ahmed Tinubu ya samu a Kotun Koli nasara ce ga dimokuraɗiyya da kuma al`ummar Najeriya.

Shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Dr Abdullahi Umar Ganduje shi ya bayyana haka a hira da BBC.

Ya ce wannan nasara ce ga Najeriya ba APC ko sauran jam’iyyu kaɗai ba.

“Ƴan siyasa sun yarda a koma ɓangaren shari’a domin bin kadinsu maimakon a tayar da yamutsi. Dole mu gode wa ƴan hamayya da kuma kowa da kowa,” in ji Ganduje.

Shugaban jam’iyyar ta APC ya ce da ma sun san nasara tasu ce saboda sun ga alamun haka tun da farko.

“Mun ƙara samun ƙwarin gwiwa da wannan nasara da muka yi a Kotun Koli,” in ji shi.

Ya ce gwamnatinsu za ta ci gaba da ayyukan raya ƙasa da ta faro ba kama hannun yaro.

Ya yi kira ga sauran jam’iyyu da ƴan takara da cewa su zo a haɗa kai wajen ciyar da ƙasa gaba.

A jiya Alhamis ne Kotun Kolin Najeriya ta tabbatar da hukuncin da kotun sauraron korafin zaɓen shugaban ƙasa ta yanke cewa Bola Tinubu ne ya samu nasara a zaɓen shugaban kasa na watan Fabrairun 2023.

vangurd 
news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp