Ƙungiyar Tarayyar Turai ta ce, ta janye jakadanta a Jamhuriyar Nijar bayan da gwamnatin mulkin sojan ƙasar ta nuna shakku kan yadda ƙungiyar ke kai agaji ga waɗanda ambaliyar ruwa ta shafa a Nijar.
A ranar Juma’a ma’aikatar harkokin wajen Nijar ta zargi ƙungiyar EU ta raba kuɗaɗe kai tsaye ga ƙungiyoyi masu zaman kansu, maimakon bi ta hannun hukumomin da ke sa ido kan yadda ake raba tallafin.
Hukumomin na Nijar sun zargi jakadan na EU a ƙasar, Salvador Pinto Da Franca da almubazzaranci da kuɗaɗen.
Tun bayan juyin mulkin da ya hamɓarar da shugaba Mohamed Bazoum a shekarar da ta gabata ake samun ƙaruwar takun saƙa tsakanin ƙasar da ƙungiyar ta EU.
Shugabannin sojin ƙasar sun juya wa tsohuwar uwargijiyarsu – Faransa – baya, sannan suka rage ƙawance ga ƙasashen Turai.