Gwamna Dauda Lawal na jihar Zamfara, ya haramta ayyukan hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba, ya kuma umarci jami’an tsaro da su dauki tsattsauran mataki kan masu karya doka.
Gwamnan a cikin wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yada labarai Suleiman Bala Idris ya fitar, ya ce lokaci ya yi da za a kawo karshen ayyukan barna ta hanyar aiwatar da matakan kare rayukan al’umma a jihar.
Ya jaddada cewa an bai wa jami’an tsaro umarnin daukar kwakkwaran mataki tare da harbe duk wanda aka samu yana aikin hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba.
“Wannan umarni ya zama dole don tabbatar da tsaro da tsaron mutanen Zamfara da kuma hana masu aikata miyagun laifuka aikata irin wadannan ayyuka.
“Haka kuma wani mataki ne na gaggawa don baiwa Gwamnatin Jiha damar kula da dukiyar jihar baki daya tare da dakile ayyukan da ke barazana ga rayuka da dukiyoyin jama’a.
“Babu shakka, hako ma’adinai ba bisa ka’ida ba na daya daga cikin ’yan bindigar da suka addabi jihar Zamfara. Dole ne mu dauki matakin gaggawa don dakile wannan matsala tare da dawo da zaman lafiya da tsaro a cikin al’ummominmu,” inji shi.